Wasanni 5 da suka sanya Manchester City ta lashe gasar Firimiya a bana

Wasanni 5 da suka sanya Manchester City ta lashe gasar Firimiya a bana

A Yammacin yau na Lahadi, 12 ga watan Mayun 2019, aka karkare wasannin gasar cin kofin firimiya na bana a Ingila. Kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ce ta sake lashe gasar karo na biyu a jere kenan ba tare da wata kungiyar ta iya lakace ma ta hanci ba.

Wasanni 5 da suka sanya Manchester City ta lashe gasar Firimiya a bana
Wasanni 5 da suka sanya Manchester City ta lashe gasar Firimiya a bana
Asali: Twitter

Bayan lallasa kungiyar Brighton Albion ci hudu da daya, kungiyar Manchester ta sha da kyar na lashe gasar firimya da maki daya rak a tsakanin ta da kungiyar kwallon kafa ta Liverpool da ke biye a bayan ta.

Shafin wasanni na jaridar AFP ya bayyana cewa, akwai wasu manyan wasanni biyar da suka taka rawar gani wajen dankawa kungiyar Manchester City nasara a bana wanda fitaccen mai horas da 'yan wasa ke rike da ita wato Pep Guardiola.

KARANTA KUMA: A shekarar 2023 zan janye jiki daga majalisar dattawa - Ekweremadu

Ga jerin manyan wasanni biyar da suka sanya kungiyar Manchester City ta zamto zakara a bana kamar haka;

Manchester City 2 - Liverpool 1

Manchester City 6 - Chelsea 0

Manchester City 1 - Tottenham 0

Manchester United 0 - Manchester City 2

Manchester City 1 - Leicester City 0

Sanarwa: Ku ci gaba da kasancewa tare da mu yayin da shafin Naij.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.android&pid=solomonovlink

Domin shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Ku biyo cikin shafukan mu na dandalan sada zumunta:

https://facebook.com/legitnghausa

https://twitter.com/legitnghausa

Ku fa'idantu da manhajar mu ta Azumi a wannan wata mai albarka a wannan shafi:

https://fb.gg/play/ramadan_ramadan

Asali: Legit.ng

Online view pixel