Masarautar Katsina ta nada sabon hakimin Malumfashi, galadiman Katsina
Masarautar jihar Katsina ta sanar da nadin Sadiq Mahuta a matsayin sabon galadiman Katsina, hakimin Malumfashi.
Sanarwar na kunshe ne cikin wata takarda da ta fito daga fito daga masarautar Katsina a ranar Talata, 30 ga watan Afrilu, 2019.
A cikin sanarwar, masarautar ta tabbatar wa Sadiq Mahuta, tsohon alkalin alkalai na jihar Katsina, nadinsa a matsayin sabon galadiman Katsina kuma hakimin Malumfashi.
Nadin Sadiq Mahuta ya biyo bayan mutuwar marigayi mai Shari'a Mamman Nasir, wanda ya rasu a cikin wannan wata da muke ciki.
A cikin takardar sanarwar da aka rabawa manema labarai, wadda magatakardan masarautar Katsina kuma sallaman masarautar, Alhaji Bello Mamman Ifo, ya sanya wa hannu.
DUBA WANNAN: Dogara ya bukaci a kama shugaban hukumar RMAFC
Da yake tabbatar da nadin, Ifo ya ce mai martaba Sarkin Katsina, Abdulmuminu Kabir, ya amince da nadin Sadiq Mahuta a matsayin Sabon Galadiman Katsina daga ranar Litinin, 30 ga watan Afrilu, 2019.
Yanzu Sadiq Mahuta ya zama daya daga cikin hakimai masu karaga (wadanda keda hannu a nada Sabon Sarki).
Za a Saka ranar da za a yi bikin nadin sarautar nan gaba kadan.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng