Tuna baya: Abubuwan da Sa'adu Zungur ya fada a kan makomar arewa shekaru 61 da suka wuce
A yayin da arewacin Najeriya ke fama da kalubale daban-daban da suka hada da na tsaro, tabarbarewar tarbiyya da lalacewar tattalin arziki, Legit.ng tayi waiwaye domin kawo maku kalaman fasihin mawaki, Marigayi Sa'adu Zungur, a cikin daya daga cikin waken sa mai taken: 'Arewa Jamhuriyya Ko Mulukiyya? ".
Sa’adu Zungur (1914-- 1958): Arewa Jamhuriya Ko Mulukiya?
- “Matukar a arewa da karuwai,
‘Yan daudu da su da Magajiya.
- Da samari masu ruwan kudi,
Ga mashaya can a gidan giya.
- Matukar ’ya’yan mu suna bara,
Titi da Loko-lokon Nijeriya.
- Hanyar birni da na kauyuka,
Allah baku mu samu abin miya.
- Sun yafu da fatar bunsuru,
Babu mai taryonsu da dukiya.
- Babu shakka’ yan kudu za su hau,
Dokin mulkin Nijeriya.
- In ko ’yan kudu sunka hau,
Babu sauran dadi, dada kowa zai
sha wuya.
- A Arewa zumunta ta mutu,
Sai karya sai sharholiya.
- Camfe-camfe da tsibbace tsibbacen,
Malaman karya ’yan damfara.
- Sai karya sai kwambon tsiya,
Sai hula mai annakiya.
- Ga gorin asali da na dukiya,
Sai kace dan annabi fariya.
DUBA WANNAN: Abun kunya: An bawa hammata iska tsakanin Abdullahi Abbas da Kwankwaso
- Jahilci ya ci lakar mu duk,
Ya sa mana sarka har wuya.
- Ya sa mana ankwa hannuwa,
Ya daure kafarmu da tsarkiya.
- Bakunan mu ya sa takunkumi,
Ba zalaka sai sharholiya.
- Wagga al’umma mai za ta yo,
A cikin zarafofin duniya.
- Kai Bahaushe ba shi da zuciya,
Za ya sha kunya nan duniya.
- “Mu dai hakkin mu gaya muku,
Ko ku karba ko ku yi dariya.
- Dariyar ku ta zam kuka gaba,
da nadamar mai kin gaskiya.
- Gaskiya ba ta neman ado,
Ko na zakin muryar zabiya.
- Karya ce mai launi bakwai,
Ga fari da baki ga rawaya.
- Ga kore ga kuma algashi,
toka-toka da ja sun garwaya”.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng