Kannywood: Nafisa Abdullahi ta soki Buhari a kan kashe-kashen Zamfara

Kannywood: Nafisa Abdullahi ta soki Buhari a kan kashe-kashen Zamfara

- Jarumar Kannywood, Nafisa Abdullahi ta nuna bacin ranta kan yadda shugaba Buhari ya ke fifita matsalolin kudu a kan na Arewa

- Jarumar tayi wannan korafin ne a lokacin da Shugaba Buhari ya yi magana a kan kisar wani matashi a Legas mai suna Kolade Johnson da yan sanda suka kashe

- Nafisa Abdullahi ta ce shugaba Buhari baya nuna damuwarsa a kan kashe-kashen Zamfara da sauran jihohin Arewa amma idan abinda ya shafi 'yan kudu ne yana bashi muhimmanci

Kannywood: Jaruma Nafisa tayi kaca-kaca da Buhari a kan kashe-kashen Zamfara
Kannywood: Jaruma Nafisa tayi kaca-kaca da Buhari a kan kashe-kashen Zamfara
Asali: Twitter

Fitacciyar jaruman Kannywood, Nafisa Abdullahi tayi kaca-kaca da shugaban kasa Muhammadu Buhari a kan rashin cewa komai a kan kashe-kashen da akeyi a wasu kauyukan jihohin Zamfara.

Jarumar ta soki shugaba Buhari a bisa maganan da ya yi a kan kisar wani matashi, Kolade Johnson da wasu 'yan sanda biyu suka kashe a Legas amma bai ce uffan ba a kan kisan kiyashin da 'yan bindiga su ke yiwa al'umma a Zamfara.

DUBA WANNAN: Yadda PDP ke kokarin hana Lawan zama shugaban majalisar dattawa - Majiyar APC

"An kashe daruruwa ko dubban mutane a Zamfara da wasu sassan Arewa kafin kisar Kolade amma ba ka yi magana a kai ba ... ina tsamanin kana tsaron yin maganar ne amma tunda wannan a kudu ya faru, tuni har kayi magana a kai." Kamar yadda Nafisa ta rubuta a Twitter.

Nafisa tayi rantsuwa cewa al'ummar Najeriya ne suke janyo matsalar da ake fama dashi a kasar, "Ana kashe mutanen ka a kasarka. Ba za kayi magana a kansa ba amma ka na nuna alhinin ka bisa rasuwar wani da ke wata bangare na duniya da bai damu da kai ba kuma watakila baya bukatar "

Jarumar ta ce ba ta fatan a rika kashe wasu mutanen, "amma abin lura a anan shine, ko sun damu da halin da ka ke ciki da matsalolin da ke damun ka? Ko sun san kana rayuwa ma?

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164