MBS na kasar Saudiyya ya warware zare da abawa a kan rahoton sayen Manchester

MBS na kasar Saudiyya ya warware zare da abawa a kan rahoton sayen Manchester

Yarima mai jiran gadon sarautar kasar Saudiyya, Mohammed Bin Salma da ake wa lakabi da ‘MBS’, ya musanta rahotanni da ke yawo a kafafen yada labarai a kan cewar yana shirin kasha kudin kasar Ingila Yuro 3.8bn domin sayen kungiyar kwallon kafa ta Manchester United.

An fara yada jita-jitar cewar Yarima MBS na son sayen kungiyar kwallon kafa ta Machester da ke kasar Ingila a watan Oktoba na shekarar 2018.

Sabuwar jita-jitar sayen kungiyar kwallon kafar ya kara bulla a kafafen yada labarai da sada zumunta a karshen makon jiya.

Kafafen yada labarai da dama sun rawaito cewar Yarima MBS na shirin sayen kungiyar Man. United a kan zunzurutun kudin kasar Ingila da yawan su ya kai Yuro biliyan 3.8.

MBS na kasar Saudiyya ya warware zare da abawa a kan rahoton sayen Manchester
Yarima MBS na kasar Saudiyya da Vladimir Putin na kasr Rasha
Asali: Depositphotos

Tun a watan Mayu na shekarar 2005 wasu ‘yan kasuwa ‘yan asalin kasar Amurka su ka mallaki hannun jari ma fi rinjaye na kungiyar Manchester United a kan kudin kasar Ingila Yuro miliyan 790.

Turki Al-shabanah, kakakin Yarima MBS ya tabbatar da cewar babu gaskiya a cikin rahotannin da ke bayyana cewar mai gidan na san a shirin sayen kungiyar kwallon kafa ta Manchester United.

DUBA WANNAN: Zabe: ‘Yan sanda sun kama wani mutum da kuri’un bogi a Sokoto

A cewar Al-shabanah; “babu gaskiya a cikin rahotannin da ke danganta Yarima MBS da niyyar sayen kungiyar kwallon kafa ta Manchester United.

Sannan ya kara da cewa; “kungiyar Manchester United ta gudanar da wani taro domin kafa wani asusun tsimi da tanadi domin ma su sha’awar saka hannun jari su zuba kudi da za a ke amfani da su wajen gudanar da harkokin kungiyar sannan a raba riba tare da su. A kan wannan maganar aka tsaya kuma har yanzu ba a cimma wata matsaya ba.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng