Masu juna biyu 30 ke mutuwa a Zamfara kulli yaumin - Kungiyar Likitocin Najeriya

Masu juna biyu 30 ke mutuwa a Zamfara kulli yaumin - Kungiyar Likitocin Najeriya

- Likitoci 345 kacal jihar Zamfara ke da shi

- Babu kayayyakin aiki a asibitocin jihar, game da cewar Dr Batur

Akalla mata masu juna biyu 30 ke mutuwa kowace rana a jihar Zamfara, mataimakin shugaban kungiyar likitocin Najeriya, Dr Mannir Bature, ya laburta.

Dakta Bature ya bayyana hakan ne a taron lakca da kungiyar Advocay Nigeria ta shirya domin inganta rayuwan matada yara a jihar Zamfara. Ya alakanta mutuwan mata da yara a jihar da rashin ingantaccen kiwon lafiya a jihar

Yace: "A jihar Zamfara a yau, yawan mutane sama da miliyan hudu, likita daya ke kula da mutane 1000 sabanin bukatar kungiyar kiwon lafiyan duniya."

Ya ce jihar na da likitoci 345 a jihar gaba dayanta. Birnin Gusau mai yawan mutane 600,000 na da likitoci 275 kacal yayinda sauran kananan hukumomin 13 na raba likitoci 75.

KU KARANTA: Dan majalisa ya fice da APC

Yayinda yake magana kan kayan aiki a asibitocin jihar, Dakta Bature yace babu asibitin jihar Zamfara dake da na'urori nebulizer, oxygen, suction da na daukan hoto.

Yace: "Babu sashen kula da kananan yara a dukkan asibitocin jihar kuma an daina inganta ma'aikata ta hanyar turasu horo."

"Wasu abubuwan dake dakile cigaban kiwon lafiya a jihar shine rashin kyakkyyawan albashi ga ma'aikata da kuma rashin basu karfin guiwa."

Shi yasa duk lokacin da aka alanta neman ma'aikatan asibiti a asibitin gwamnatin tarayya, za ka ga ma'aikatan jihar Zamfara suna guduwa."

Sanarwa: Shafin Naij.com Hausa shine yanzu ya koma Legit.ng Hausa, don inganta muku zafafan labarai dama kayatarwa

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng