INEC ta fitar da sunayen 'yan takarar da za su fafata a zaben maye gurbi a jihohin arewa 3

INEC ta fitar da sunayen 'yan takarar da za su fafata a zaben maye gurbi a jihohin arewa 3

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta saki sunayen 'yan takara da jam'iyyun su a zaben maye gurbi na ranar 17 ga wata da za a yi a jihohin Katsina, Bauchi, da Kwara.

INEC ta saki sunayen ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Festus Okoye, kwamishinan hukumar mai kula da bangaren yada labarai da ilimantar da ma su kada kuri'a.

Za a yi zaben maye gurbin ne a mazabar Kankia/Kusada/Ingawa a jihar Katsina, mazabar Toro a jihar Bauchi, mazabar Ekiti/Irepodun/Isin/Oke-Ero a jihar Kwara, da kuma mazabar Ikom II a jihar Kuros Riba.

Zabe maye gurbi a jihohin arewa 3: INEC ta fitar da sunayen 'yan takara da jam'iyyun su
Zabe maye gurbi a jihohin arewa 3: INEC ta fitar da sunayen 'yan takara da jam'iyyun su
Asali: UGC

INEC ta bayyana cewar jam'iyyu hudu ne su ka mika sunayen 'yan takarar su daga jihar Katsina.

DUBA WANNA: Wani mutum ya datse kan shugaban matasa a karamar hukumar Oshiomhole

'Yan takara su ne Nasiru Kankia na jam'iyyar PRP, Abdullahi Umar na jam'iyyar YES, Abdulsamad Abdullahi na jam'iyyar PDP, da Abubakar Kusada na jam'iyyar APC.

A mazabar Toro ta jihar Bauchi akwai; Shehu Umar na jam'iyyar PDP da Yusuf Nuhu na jam'iyyar APC.

Daga mazabar Ekiti Irepodun/ Isin /Oke-Ero a jihar Kwara akwai Femi Ara na jam'iyyar LP, Olaniyan Ayorinde, na jam'iyyar UPN, Jimoh Damilare na PDP da kuma Ajayi Bidemi na APC.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng