Babban Sarki a Najeriya ya bukaci Ingila ta dawo da kayan tarihin masarautar sa

Babban Sarki a Najeriya ya bukaci Ingila ta dawo da kayan tarihin masarautar sa

Sarkin Benin, Ewuare II, ya bukaci yariman kasar Wales, Charles George, da ke ziyara a Najeriya, da ya saka baki domin ganin kasar Ingila ta dawowa da masarautar sa kayan tarihin da ta kwasa a shekarar 1857.

Sarkin ya bayyana cewar dawo ma sa da kayan tarihin zai bashi damar gina gidan tarihi da zai bunkasa tarihi da yawon bude ido a birnin Benin, jihar Edo.

Ewure II na wadannan kalamai ne a cikin wani jawabi da ya gabatar yayin ganawa da yarima mai jiran gadon sarautar kasar Ingila a wani taro da su ka yi jiya a gidan jakadancin kasar Ingila da ke unguwar Maitama a Abuja.

Ragowar sarakunan gargajiya da su ka halarci taron sun hada da Sarkin kasar Ife, Enitan Ogunwusi; Sarkin Musulmi, Sa'ad Abubakar; Sarkin Onitsha, Igwe Alfred; Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, da sauran su.

Babban Sarki a Najeriya ya bukaci Ingila ta dawo da kayan tarihin masarautar sa
Prince Charles da sarakunan Najeriya
Asali: UGC

Yarima Charles, ya ziyarci shugaba Buhari kafin ganawa da sarakunan na gargajiya a cigaba da ziyarar kasashen Afrika da su ka hada da Gambia, Ghana, da Najeriya.

Sarkin na Benin ya yi waiwaye a kan kyakykyawar dangantakar da ke tsakanin masarautar sa da ta kasar Ingila tare da bayyana irin zumunci da fahimtar juna da ke tsakanin su.

DUBA WANNAN: An bawa Hadiza Gabon kyautar dankareriyar mota, hoto

Sarkin ya shaidawa manema labarai cewar sun tattauna a kan batutuwan da su ka shafi tsaro, matsalar safarar mutane da kuma ilimin 'ya'ya mata.

Kazalika, Sarkin Kano ya ce sun tattauna a kan matsalolin da su ka shafi yanayi da muhalli, yadda za a shawo kan yawon jama'a da matsalar da za a iya fuskanta idan ba a yi hakan ba.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng