Rundunar soji sun kama shanaye da aka sace a Taraba

Rundunar soji sun kama shanaye da aka sace a Taraba

- Sojoji sun cafke wani babban mota cike da shanaye na sata

- Sun kama shanayen da yawansu ya kai 52 a wani kauyen jihar Taraba

- Hakan ya biyo bayan rikicin da ya kaure a yankin kwanan nan

Rundunar sojin Najeriya tace ta cafke wani babban mota cike da shanaye na sata a kauyen Nyabai dake jihar Taraba.

An tattaro cewa anyi fashin Shanayen wanda adadinsu ya kai 52 daga karamar hukumar Lau, bayan rikicin da ya barke a yankin kwanakin baya.

Rundunar soji sun kama shanaye da aka sace a Taraba
Rundunar soji sun kama shanaye da aka sace a Taraba
Asali: Twitter

A cewar sojojin an mika shanayen ga rundunar yan sanda domin ci gaba da bin cike don gano mamalakan shanun.

KU KARANTA KUMA: Doka ta fara aiki: Mutane 5 na rufe a hannun yan sanda kan laifin tallata naira

A wani hiran wayar tarho, kakakin yan sandan jihar, David Misal yace bai samu kowani rahoto game da kamun ba tukuna.

An kai shanayen gonan gwamnatin jihar domin kula da su a tsanaki zuwa lokacin da masu shi zasu bayyana.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin Legit.ng Hausa zai koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewar ku tare da mu.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng