'Yan sanda sun damke 'yan bangar siyasa da suka addabi mutane a Kano (Hotuna)

'Yan sanda sun damke 'yan bangar siyasa da suka addabi mutane a Kano (Hotuna)

- Yan sanda sun kama wasu 'yan bangan siyasa da suke nemi tayar da tsaye yayin zabukkan fidda gwani a jihar Kano

- An same 'yan bangar da makamai kamar adda, sanduna, wukake, barandami da sauransu

- Hukumar 'yan sanda ta ce za'a mika su zuwa kotu da zarar an kammala bincike domin su fuskanci shari'a

A yau Juma’a ne rundunar ta 'yan sanda reshen jihar Kano ta yi gabatarwa manema labarai wasu 'yan bangar siyasa wadanda aka kama a yayin zabubbukan fidda gwani na jam’iyyu daga Talata 2 zuwa Juma’a 5 ga watan Oktoban 2018.

'Yan sanda sun cika hannunsu da 'yan bangar siyasa da suka adabi mutane a Kano
'Yan sanda sun cika hannunsu da 'yan bangar siyasa da suka adabi mutane a Kano
Asali: Facebook

DUBA WANNAN: 'Yan takarar shugabancin kasa na PDP 5 ne kawai suka hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya

Cikin wadanda aka kama har da wani dan fashi da makami wanda an dade ana nemansa wato Bashir Musa da aka fi sani da Gachi wanda ke addabar Unguwannin Hotoro, Na'ibawa, Mariri da sauransu a birnin Kano.

'Yan sanda sun cika hannunsu da 'yan bangar siyasa da suka adabi mutane a Kano
'Yan sanda sun cika hannunsu da 'yan bangar siyasa da suka adabi mutane a Kano
Asali: Facebook

'Yan sanda sun cika hannunsu da 'yan bangar siyasa da suka adabi mutane a Kano
'Yan sanda sun cika hannunsu da 'yan bangar siyasa da suka adabi mutane a Kano
Asali: Facebook

Kakakin rundunar yansandan jihar Kano, SP Magaji Musa Majia ya ce sun kama 'yan bangar siyasar da mugayen makamai masu yawa da suka hada da adda, barandami, sanduna da wukake. Yace dukkanin yandaban da ke hannun su zasu mika su zuwa kotu domin ayi musu hukunci dai dai da abinda suka aikata.

'Yan sanda sun cika hannunsu da 'yan bangar siyasa da suka adabi mutane a Kano
'Yan sanda sun cika hannunsu da 'yan bangar siyasa da suka adabi mutane a Kano
Asali: Facebook

Daga karshe SP Majia, ya tabbatar da cewa rundunarsu za ta cigaba da aiki ba dare ba rana wajen kame duk wasu 'yan bangar siyasa a Jihar Kano don ganin anyi zaben shekara ta 2019 cikin lafiya da kwanciyar hankali.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin Legit.ng Hausa zai koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164