Ziyarar Theresa May: Gwamnatin Ingila tayi furuci a kan takarar Buhari da APC ba zata so ba

Ziyarar Theresa May: Gwamnatin Ingila tayi furuci a kan takarar Buhari da APC ba zata so ba

- A kwanakin baya-bayan nan ne Firaminstar kasar Ingila, Theresa May, ta kawo wata ziyarar aiki Najeriya

- Ziyarar ta Theresa May ta jawo barkewar cece-kuce a tsakanin manyan jam’iyyun Najeriya, musamman tsakanin APC mai mulki da PDP, mai adawa

- A yau, Litinin, gwamnatin kasar Ingila, ta hannun ofishin jakadancinta dake Najeriya, tayi Karin haske, domin cireshakku a kan batun ziyarar ta Firaminsta May

Babban ofishin jakadancin kasar Ingila dake Najeriya y ace ziyarar da firaminastar kasar, Theresa May, ta kawo kwanakin baya bat a da alaka da nuna goyon baya ga takarar shugaba Buhari ko wani dan takara.

Laura Beaufils, mataimakiyar jakadan kasar Ingila a Najeriya, ce ta bayyana hakan yau a Legas yayin amsa tambayoyi daga manema labarai.

Ziyarar Theresa May: Gwamnatin Ingila tayi furuci a kan takarar Buhari da APC ba zata so ba
Theresa May da Buhari
Asali: UGC

Laura ta jaddada niyyar kasar Ingila ta kasha Yuro miliyan #47.4 domin karfafa dimokradiyya a Najeriya karkashin manufar kasar na karawa siyasa karfi a Najeriya zagaye na 2 (DDiN2).

DUBA WANNAN: Sule Lamido ya lissafa mutane 4 da suka fi Buhari kima da gaskiya

Da ta ke bayani a kan rawar da kasar Ingila ke takawa domin karfafa harkokin siyasa a Najeriya, Laura, ta ce gwamnatin Birtaniya ba tad a niyyar canja zabin mutanen Najeriya a zabukan shekarar 2019.

Wannan mataki ya yiwa wani bangare na masu son yin takarar shugaban dadi, musamman bangaren ‘yan takarar jam’iyyar PDP dake ganin cewar gwamnatin Ingila ta karkata a kan takarar shugaba Buhari.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng