Jerin tsaffin Gwamnoni 15 dake rike da Kujeru a Majalisar dattawa

Jerin tsaffin Gwamnoni 15 dake rike da Kujeru a Majalisar dattawa

A yau tankade da rairayen jaridar Legit.ng ya kawo ma ku jerin tsaffin gwamnonin da suke rike da madafan iko kan kujerun Sanatoci a majalisar dattawan kasar nan, bayan da suka kammala wa'adin su a kujerun gwamnoni na jihohin su.

Jerin tsaffin Gwamnoni 15 dake rike da Kujeru a Majalisar dattawa
Jerin tsaffin Gwamnoni 15 dake rike da Kujeru a Majalisar dattawa
Asali: UGC

A makon da ya gabata jaridar ta Legit.ng ta kawo mu ku jerin sunayen gwamnonin jihohin kasar nan ma su ci a karkashin jam'iyyar APC.

Binciken jaridar ya bayyana cewa a halin yanzu akwai tsaffin gwamnoni 15 da ke rike da kujerun Sanatoci a majalisar dattawa.

Ga jerin sunayen tsafaffin gwamnonin tare da mazabar da suke wakilta a majalisar dattawa kamar haka:

1. Abubakar Bukola Saraki; Sanatan jihar Kwara ta Tsakiya

2. Rabi'u Musa Kwankwaso; Sanatan jihar Kano ta Tsakiya

3. Kabiru Gaya; Sanatan jihar Kano ta Kudu

4. Godswill Akpabio; Sanatan jihar Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma

5. Aliyu Magatakarda Wamakko; Sanatan Jihar Sakkwato ta Arewa

6. Abdullahi Adamu; Sanatan jihar Nasarrawa ta Yamma

7. Sam Egwu; Sanatan jihar Ebonyi ta Arewa

8. Muhammad Shaaba Lafiagi; Sanatan jihar Kwara ta Arewa

KARANTA KUMA: Rikici a PDP yayin da amintattun jam'iyya ke bayyana goyan bayan su ga wasu 'yan takara na jam'iyyar

9. Joshua Chibi Dariye; Sanatan jihar Filato ta Tsakiya

10. Jonah Jang; Sanatan jihar Filato ta Arewa

11. Ahmed Sani Yerima; Sanatan jihar Zamfara ta Yamma

12. Danjuma Goje; Sanatan jihar Gombe ta Tsakiya

13. Bukar Abba Ibrahim; Sanatan jihar Yobe ta Gabas

14. George Akume; Sanatan jihar Benuwe ta Yamma

15. Theodore Orji; Sanatan jihar Abia ta Tsakiya

Kazalika akwai kuma wasu tsofaffin mataimakan gwamna dake rike da kujeru a majalisar dattawa da suka hadar da; Mrs Biodun Olujimi ta jihar Ekiti da kuma Enyinaya Abaribe na jihar Abia.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Domin shawara ko bamu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku duba shafukanmu na dandalin sada zumunta a:

https://business.facebook.com/pg/naijcomhausa

https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng