Jerin tsaffin Gwamnoni 15 dake rike da Kujeru a Majalisar dattawa

Jerin tsaffin Gwamnoni 15 dake rike da Kujeru a Majalisar dattawa

A yau tankade da rairayen jaridar Legit.ng ya kawo ma ku jerin tsaffin gwamnonin da suke rike da madafan iko kan kujerun Sanatoci a majalisar dattawan kasar nan, bayan da suka kammala wa'adin su a kujerun gwamnoni na jihohin su.

Jerin tsaffin Gwamnoni 15 dake rike da Kujeru a Majalisar dattawa
Jerin tsaffin Gwamnoni 15 dake rike da Kujeru a Majalisar dattawa
Asali: UGC

A makon da ya gabata jaridar ta Legit.ng ta kawo mu ku jerin sunayen gwamnonin jihohin kasar nan ma su ci a karkashin jam'iyyar APC.

Binciken jaridar ya bayyana cewa a halin yanzu akwai tsaffin gwamnoni 15 da ke rike da kujerun Sanatoci a majalisar dattawa.

Ga jerin sunayen tsafaffin gwamnonin tare da mazabar da suke wakilta a majalisar dattawa kamar haka:

1. Abubakar Bukola Saraki; Sanatan jihar Kwara ta Tsakiya

2. Rabi'u Musa Kwankwaso; Sanatan jihar Kano ta Tsakiya

3. Kabiru Gaya; Sanatan jihar Kano ta Kudu

4. Godswill Akpabio; Sanatan jihar Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma

5. Aliyu Magatakarda Wamakko; Sanatan Jihar Sakkwato ta Arewa

6. Abdullahi Adamu; Sanatan jihar Nasarrawa ta Yamma

7. Sam Egwu; Sanatan jihar Ebonyi ta Arewa

8. Muhammad Shaaba Lafiagi; Sanatan jihar Kwara ta Arewa

KARANTA KUMA: Rikici a PDP yayin da amintattun jam'iyya ke bayyana goyan bayan su ga wasu 'yan takara na jam'iyyar

9. Joshua Chibi Dariye; Sanatan jihar Filato ta Tsakiya

10. Jonah Jang; Sanatan jihar Filato ta Arewa

11. Ahmed Sani Yerima; Sanatan jihar Zamfara ta Yamma

12. Danjuma Goje; Sanatan jihar Gombe ta Tsakiya

13. Bukar Abba Ibrahim; Sanatan jihar Yobe ta Gabas

14. George Akume; Sanatan jihar Benuwe ta Yamma

15. Theodore Orji; Sanatan jihar Abia ta Tsakiya

Kazalika akwai kuma wasu tsofaffin mataimakan gwamna dake rike da kujeru a majalisar dattawa da suka hadar da; Mrs Biodun Olujimi ta jihar Ekiti da kuma Enyinaya Abaribe na jihar Abia.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Domin shawara ko bamu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku duba shafukanmu na dandalin sada zumunta a:

https://business.facebook.com/pg/naijcomhausa

https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel