Allah ya yiwa babban malamin Izala a Kaduna rasuwa

Allah ya yiwa babban malamin Izala a Kaduna rasuwa

Allah ya yiwa daya daga cikin malaman izala kuma limamin masallacin juma’a na NNDPC dake garin Kaduna, Sheikh Abubakar Baban Tune, rasuwa a yau, Lahadi, a asibitin shika na garin Zaria.

An yi jana’zar malamin da Magriba a masallacin unguwar Low Cost dake garin Zaria, kamar yadda fitaccen malami, Sheikh Ahmad Abubakar Gumi, ya sanar a shafinsa na Facebook. •

Muna addu'ah Allah Ta'ala Ya Jikan Malamin mu Sheikh Abubakar Baban Tune (Babban Limamin Masallacin Juma'ah na NNPC Kaduna) Ya rasu Yau Litinin 30 Dhul Hajj, 1439H, 10 Sept, 2018 a Asibitin Shika, Zaria.

Allah ya yiwa babban malamin Izala a Kaduna rasuwa
Marigayi Sgheikh Abubakar
Asali: Facebook

Za'ayi Jana'iza da Magriba a Masallacin Low coast dake Zaria.

Allah Ta'ala Ya Jikansa da Rahama Ya gafarta masa Yasa Mutuwa ta zama Hutu a gare shi, Ya karbi ayyukan sa na alkhairi, na kuskure Kuma Allah Ya yafe, Allah yasa tamu tayi kyau bayan tasu. Amin,” kamar yadda Sheikh Gumi ya rubuta a sahafinsa na Facebook

DUBA WANNAN: 2019: Tsohon IG, Sulaiman Abba, ya yanki fam din takarar sanata a APC

A wani labarin na Legit.ng, kun ji cewar gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya halarci bikin bude wata makarantar Islamiyya a unguwar Kaura dake garin Zaria, a jiya Lahadi.

Tsohon jakadan Najeriya a kasar Ingila, Dalhatu Sarki Tafida, ne ya gayyaci gwamna El-Rufa'i bikin bude makarantar da aka gina domin tunawa da marigayi Malam Abubakar Magatakarda Tafida( Baba Maidoki).

Makarantar zata bawa ilimin mata muhimmanci, a bangaren addinin Islama da na boko.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng