El-Rufa’i ya halarci bikin bude Islamiyya da jigo a PDP ya gina a Zaria, hotuna

El-Rufa’i ya halarci bikin bude Islamiyya da jigo a PDP ya gina a Zaria, hotuna

Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya halarci bikin bude wata makarantar Islamiyya a unguwar Kaura dake garin Zaria, a jiya Lahadi.

Tsohon jakadan Najeriya a kasar Ingila, Dalhatu Sarki Tafida, ne ya gayyaci gwamna El-Rufa'i bikin bude makarantar da aka gina domin tunawa da marigayi Malam Abubakar Magatakarda Tafida( Baba Maidoki).

Makarantar zata bawa ilimin mata muhimmanci, a bangaren addinin Islama da na boko.

El-Rufa’i ya halarci bikin bude Islamiyya da jigo a PDP ya gina a Zaria, hotuna
El-Rufa’i na gaisawa da sarkin Musulmi mai alfarma, Sa'ad Abubakar II.
Asali: Facebook

El-Rufa’i ya halarci bikin bude Islamiyya da jigo a PDP ya gina a Zaria, hotuna
Sarkin Muslmi yayin kaddamar da makarantar Islamiyya
Asali: Facebook

Mai alfarma sarkin musulmi, Abubakar Sa’ad II, ne ya kasance bako na musamman a wurin taron bude makarantar.

Wanda ya gina makarantar, Dalhatu Sarki Tafida, jigo ne a jam'iyyar PDP.

DUBA WANNAN: Manyan Najeriya sun halarci bikin diyar ministan Buhari

Ya taba zama Sanata a PDP kafin daga bisani gwamnatin jam'iyyar ta tura shi kasar Ingila a matsayin jakadan Najeriya.

El-Rufa’i ya halarci bikin bude Islamiyya da jigo a PDP ya gina a Zaria, hotuna
El-Rufa’i ya halarci bikin bude Islamiyya a Zaria
Asali: Facebook

El-Rufa’i ya halarci bikin bude Islamiyya da jigo a PDP ya gina a Zaria, hotuna
El-Rufa’i ya halarci bikin bude Islamiyya a Zaria
Asali: Facebook

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng