Duba da kan ka: Hukumar zabe ta saki sakamakon zaben kananan hukumomin jihar Imo

Duba da kan ka: Hukumar zabe ta saki sakamakon zaben kananan hukumomin jihar Imo

A yau ne hukumar zabe a Imo ta saki ilahirin sakamakon zaben kananan hukumomin jihar da aka kammala a jiya, Asabar.

Jam'iyyar APC mai mulki a jihar ta Imo ce ta lashe zaben a fadin kananan hukumomi 27 da jihar ta Imo ke da su.

Ethelbert Ibebuchi, shugaban hukumar zabe ta Imo, ne ya sanar da hakan a yau, Lahadi, a Owerri, babban birnin jihar.

Duba da kan ka: Hukumar zabe ta saki sakamakon zaben kananan hukumomin jihar Imo
Duba da kan ka: Hukumar zabe ta saki sakamakon zaben kananan hukumomin jihar Imo

DUBA WANNAN: 2019: Dan takarar PDP ya yi tsokaci kan farin jini Buhari a arewa

A cewar wasu rahotanni, jam'iyyun adawa na PDP da APGA sun kauracewa zaben.

Ba wani bakon abu bane jam'iyyar dake da gwamnati a jiha ta lashe dukkan kujerun takara a zaben kananan hukumomi.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng