PDP tayi watsi da sakamakon zaben Ekiti, duba hotunan da ta saki a matsayin shaidar magudi

PDP tayi watsi da sakamakon zaben Ekiti, duba hotunan da ta saki a matsayin shaidar magudi

Jam’iyyar PDP tayi watsi da sakamakon da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta sanar na zaben gwamnan jihar Ekiti da aka yi jiya. A sakamakon da INEC ta fitar, dan takarar jam’iyyar APC, Kayode Fayemi, ya sami nasara a kan dan takarar PDP, Farfesa Kolapo Olusola.

Da sanyin safiyar yau, Lahadi, ne hukumar INEC ta sanar da cewar Fayemi na APC ya samu nasara a kananan hukumomi 11 a cikin 16 dake jihar ta Ekiti. Fayemi ya samu jimillar kuri’u 197,459 yayinda Kolapo ya samu kuri’u 178,121.

Saidai a jawabin da ta fitar ta bakin kakakinta, Kola Ologbondian, ta bayyana cewar an yi masu fashin zabe da tsakar rana tare da yin watsi da sakamakon zaben gabadayansa.

PDP tayi watsi da sakamakon zaben Ekiti, duba hotunan da ta saki a matsayin shaidar magudi
Hotunan da PDP ta saki a matsayin shaidar magudi

PDP tayi watsi da sakamakon zaben Ekiti, duba hotunan da ta saki a matsayin shaidar magudi
Hotunan da PDP ta saki a matsayin shaidar magudi

PDP tayi watsi da sakamakon zaben Ekiti, duba hotunan da ta saki a matsayin shaidar magudi
Hotunan da PDP ta saki a matsayin shaidar magudi

A cewar PDP, sakamakon zaben da suke da shi daga mazabun jihar, ya nuna sune keda mafi rinjayen kuri’un da aka kada a zaben amma aka yi amfani da karfin gwamnati da jami’an tsaro aka canja sakamakon zaben.

DUBA WANNAN: Abu 4 da PDP zata yi domin dawo da martabarta a Najeriya - Obasanjo

A wasu jerin sakonni da PDP ta fitar a shafinta dake dandalin sada zumunta na Tuwita ta saki wasu hotuna(kamar yadda ku ka gani a sama) da tayi ikirarin cewar na irin magudin da aka tafka mata ne a zaben na jiya.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel