Madallah: Duba hoton wasu mutane 8 da dakarun soji suka ceto daga masu garkuwa a jihar Kaduna
A ranar Litinin da ta gabata ne dakarun sojin Najeriya dake atisayen Idon Raini domin kakkabe masu satar mutane da tayar da kayar baya suka yi nasar ceton wasu mutane 8 da masu garkuwa suka sace a kan hanyar Maganda zuwa Sofo a karamar hukumar Birnin Gwari.
Sojojin sun kwato mutanen ne yayin sintirin cigaba da kakkabe masu garkuwar da kuma aikata laifuka irin na ta’addanci a kan hanyar Maganda zuwa Funtuwa.
Daga cikin wadanda hukumar sojin ta kubutar yayin sintirin da take gudanarwa akwai maza uku (3), mata biyu (2), da kananan yara uku(3).
![Madallah: Duba hoton wasu mutane 8 da dakarun soji suka ceto daga masu garkuwa a jihar Kaduna Madallah: Duba hoton wasu mutane 8 da dakarun soji suka ceto daga masu garkuwa a jihar Kaduna](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt4te162sauo8.jpeg?v=1)
![Madallah: Duba hoton wasu mutane 8 da dakarun soji suka ceto daga masu garkuwa a jihar Kaduna Madallah: Duba hoton wasu mutane 8 da dakarun soji suka ceto daga masu garkuwa a jihar Kaduna](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt2silm8v45u1.jpeg?v=1)
Darektan hulda da jama’a na rundunar sojin Najeriya, Birgediya Janar Texas Chwukwu, y ace bayan mutanen da suka kubutar, sun yi nasar kwace wasu kayayyaki daga hannun masu garkuwar, da suka hada da; wata mota ja kirar Golf, Tirela, da kuma akwatunan kaya na matafiya.
DUBA WANNAN: Duba yadda wata motar alfarma ta rusa wani masallaci bayan ta kwace daga hannun direba
Kazalika, rundunar sojin ta ce, ta samu wani babur a kauyen Nachibi da mai shi ya gudu ya bari bayan hango ayarin sojojin na tunkaro inda suke aikata miyagun laifuka.
A kauyen Maidaro, dakarun sun fafata da wasu ‘yan binda da suka samu na gumurzu da wasu ‘yan kungiyar bijilanti yayin da suke kokarin sace shanu a kauyen.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa
Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng