Duk rana sai an fitar da Biliyan 2 domin Boko Haram a mulkin Jonathan – Naja’atu Muhammad

Duk rana sai an fitar da Biliyan 2 domin Boko Haram a mulkin Jonathan – Naja’atu Muhammad

Sai a makon nan mu ke samun labari daga Hajiya Naja’atu Muhammad cewa a duk rana ta Allah a lokacin tsohon Shugaban kasa Dr. Goodluck Jonathan yana mulki sai an fitar da Naira Biliyan 2 domin sha’anin tsaro a Najeriya.

Sanata Naja’atu Muhammad tayi wani jawabi kamar yadda mu ka samu rahoto daga Jaridar The Cable a wajen taron tunawa da Yaran Chibok da Boko Haram su ka sace a Abuja inda ta zargi manyan kasar kan rikicin Boko Haram.

Duk rana sai an fitar da Biliyan 2 domin Boko Haram a mulkin Jonathan – Naja’atu Muhammad
Tsohuwar Sanatar Kano ta tsakiya Naja’atu Muhammad

Fitacciyar ‘Yar siyasar tace Ali Mode Sheriff yana cikin wadanda su ka hura rikicin Boko Haram domin shi ya dasa su a lokacin yana Gwamna. Muhammad tace tsohon Gwamnan na Borno ya taba nada ‘Dan Boko Haram Kwamishina.

KU KARANTA: Na-kusa da Shugaban kasa Buhari yayi kaca-kaca da shi kan Boko Haram

Tsohuwar Sanatar ta Kanotace Gwamnatin Jonathan tayi amfani da wannan dama ta rika satar dukiyar kasa har Naira biliyan 2 a kowace rana amma ba a ga gyara a harkar tsaro ba. Muhammad tace an maida rikicin hanyar cin kudi a lokacin.

Ita ma dai fitacciyar ‘Yar siyasar tace Gwamnatin Najeriya tayi sakaci wajen kare rayukan jama’a ta kara da cewa babu gidan da rikicin Boko Haram bai shafa ba a Jihar Borno. A karshe ta nemi ayi wa Rundunar Sojin kasar garambawul gaba daya.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel