Cikakken jerin Gwamnonin Katsina tun daga kirkirar Jihar

Cikakken jerin Gwamnonin Katsina tun daga kirkirar Jihar

A yayin da Jihar Katsina ta cika shekaru 30 da kafuwa a Najeriya mun kawo maku jerin Gwamnonin Jihar tun daga shekarar 1987 kawo yanzu.

Cikakken jerin Gwamnonin Katsina tun daga kirkirar Jihar
Gwamnonin Jihar Katsina daga 1987 zuwa 2017

1. Kanal Abdullahi Sarki Mukhtar

Kanal Sarki Mukhtar shi ne Gwamnan farko kuma Soji da ya mulki Jihar daga Satumban 1987 zuwa Agustan 1988.

2. Kanal Lawrence Onojo

Onoja yayi mulki daga lokacin da Kanal Mukhtar ya sauka da watanni biyu zuwa karshen shekarar 1988.

3. Kanal Yahaya Madaki

Yahaya John Madawaki ya karbi ragamar mulkin bayan Onojo har zuwa shekarar 1992 lokacin da aka yi zaben siyasa.

4. Saidu Barda

Alhaji Saidu Barda ya lashe zaben Gwamna na farko a Jihar a karkashin Jam'iyyar NRC kafin a sauke Gwamnonin.

KU KARANTA: Za a shiga wani mugun yajin aiki a Jihar Kogi

5. Kyaftin E.A Acholonu

Acholonu wanda shi ma Soja ne ya karbi mulkin Jihar a lokacin Shugaba Janar Abacha bayan an sauke Gwamnoni farar hula.

6. Kanal Samaila Bature

Kanal Chama yayi mulkin sa ne daga tsakiyar 1996 bayan Acholonu har zuwa tsakiyar shekarar 1998.

7. Laftana Kanal Joseph L. Akaageger

Akaagegar yayi mulkin sa na kusan shekara guda daga 1998 zuwa 1999 lokacin da aka dawo farar hula.

8. Alhaji Umaru Yaradua

Tsohon Shugaba Ummaru Musa Yaradua ya lashe zaben 1999 a karkashin PDP inda yayi shekara 8 daga nan ya zama Shugaban kasa.

9. Ibrahim Shehu Shema

Bayan Marigayi Yaradua sai Barista Ibrahim Shema wanda shi ma tayi shekaru 8 kan karaga zuwa 2015.

10. Rt. Hon. Aminu Masari

A shekarar 2015 ne Aminu Bello Masari ya dare kujerar Gwamna a karkashin Jam'iyyar adawa ta APC.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Mahaifin Jagoran Biyafara Nnamdi Kanu yana jawabi

Asali: Legit.ng

Online view pixel