Saudiya za ta gina birnin nishadi a kusa da Riyadh

Saudiya za ta gina birnin nishadi a kusa da Riyadh

Saudiya ta na shirin gina abin da ta bayyana a matsayin birnin nishadi a wajen babban birnin kasar, Riyadh.

Saudiya za ta gina birnin nishadi a kusa da Riyadh
Saudiya za ta gina birnin nishadi a kusa da Riyadh

A shekarar 2022 ake sa ran bude birnin, a inda za a rinka bukukuwan baje kolin al'adu, da wasanni da kuma abubuwan shakatawa.

KU KARANTA KUMA: Buhari ya nada sababbin shugabannin hukumomi da ma’aikatun ma’aikatar Ilimi

Legit.ng ta rahoto cewa mataimakin yarima mai jiran gado a Saudiya, Mohammed bin Salman ya ce ana fatan birnin da za a gina, zai zama wani wuri mai muhimmanci ga raya al'adu da cimma bukatun mutane masu tasowa a kasar a gaba.

Gwamnatin Saudiya na fatan wannan shiri da ake wa lakabi da Vision 2030, zai samar da guraben ayyukan yi ga matasa a kasar, tare da yin sassauci ga wasu tsauraran ka'idoji a kasar.

Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

Bidiyon yadda matasa ke ta murna a lokacin da shugaba Buhari ya dawo Najeriya daga birnin Landan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng