Tashin hankali yayinda kudin man jirgi ya tashi N265

Tashin hankali yayinda kudin man jirgi ya tashi N265

Kudin man jirgin sama ta tashn N265 ga lita a Najeriya. Wannan na faruwa ne duk da cewa farashin kudi mai ya sauka a kasuwan duniya.

Tashin hankali yayinda kudin man jirgi ya tashi N265
Tashin hankali yayinda kudin man jirgi ya tashi N265

Wannan abu ya tayar da hankalin ma’aikatan jiragen sama kuma suna sa ran cewa wannan abu zai iya jan kulle filayen jirgin sama.

A Kano, Kaduna da wasu jihohin arewa, kudin man ya haura tsakanin N255 da N265. A legas kuma, anan sayarwa N240 zuwa N250, dangane da yawan man da mutum ke bukatan saya.

KU KARANTA: Yan PDP sunce Ali Modu Sherrif munafiki ne

Kimanin makonni 2 da suka gabata, kudin man ta a N220 a Legas, da kuma N230 a sauran wurare.

Tsakanin Junairu da Fabrairun 2016, kudin man na N120, amma cikin watanni 12, kudin ta ninka kanta.

Wani dan kasuwan mai ya tabbatar sa wannan tashin farashin ga jaridar Sahara Reporters. Majiyar ta dauran laifin wannan abu ga rattan da ke tsakanin Naira da dalar Amurka, wanda ya tashi daga N490 zuwa N506.

https://web.facebook.com/naijcomhausa/#

https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng