Ba ruwan mu da rikicin Kaduna inji fulani

Ba ruwan mu da rikicin Kaduna inji fulani

A jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya, kungiyar Fulani ta musanta zarge-zargen da wasu ke yi cewa su ne ke kai hare-hare a kudancin jahar.

Ba ruwan mu da rikicin Kaduna inji fulani
Ba ruwan mu da rikicin Kaduna inji fulani

A wani taron manema labarai a Kaduna, al'ummar Fulanin sun ce ba zaunannun Fulani na kudancin jihar ne ke kaddamar da hare hare ba, mai yiwuwa wasu Fulani ne dake zuwa yankin daga waje.

KU KARANTA KUMA: Kyakkyawan sauyi na nan tafi a 2017 inji Shugaba Buhari

A halin yanzu dai an kafa dokar hana fita ta sa'o'i 24 a wasu kananan hukumomi na jihar sanadiyyar rikice-rikice tsakanin fulanin da wasu kabilu.

Rahotanni sun ce an yi asarar rayuka da dukiyoyi a hare hare na baya bayan nan da wasu 'yan bindiga suka kaddamar a Kudancin jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng