Albashin ma'aikata
Malaman jami'a sun koka kan rashin samun albashin watan Mayu bayan kusan mako daya da karewar wata. Abdelghaffar Amoka ya ce sun shiga sallah ba albashi.
Gwamnatin jihar Jigawa ta samu nasarar tsaftace bangaren ma'aikatanta. Gwamnatin ta gudanar da bincike inda ta gano dubunnan ma'aikata na bogi da ke karbar albashi.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince a biya ma'aikata da 'yan fansho kudade don su gudanar da bukukuwan babbar Sallah a cikin walwala da jindadi.
Gwamna Fintiri ya fara biyan sabon mafi karancin albashi na N70,000 ga ma'aikatan kananan hukumomin Adamawa. Ya ware ₦5bn don biyan hakkokin masu ritaya.
Ma’aikatan shari'a karkashin JUSUN sun rufe kotuna a Ibadan, a wani mataki na yajin aiki. Sun bukaci gwamnati ta kara masu albashi da alawus da 25% da 35%.
Gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya shirya gwangwaje ma'aikata don bukukuwan babbar Sallah. Gwamnan ya umarci a biya su albashin watan Yunin 2025.
Gwamnatin Tarayya karkashin jagorancin shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ta fara biyan ma'aikata bashin N35,000 da ta masu alƙawari a watannin baya.
Ma’aikatan hukumar nukiliya sun rufe Ma’aikatar Kudi a Abuja saboda bashin albashi da alawus, sun zargi minista da hana su hakkokinsu duk da roƙon da suka yi.
Gwamna Francis Nwifuru ya ƙara albashi ga sababbin likitoci zuwa N500,000, ya kuma kaddamar da shirin samar da magunguna a farashi mai rahusa a jihar Ebonyi.
Albashin ma'aikata
Samu kari