Albashin ma'aikata
Yan kwadago sun daidaita da gwamnatin Cross River wajen karin albashi zuwa N7,000. Lamarin ya zo ne a lokacin da yan kwadago ke shirin fara yajin aiki a jihar.
Ƙungiyar NLC reshen jihar Sokoto ta fasa shiga yajin aikin da aka shirya gudanarwa kan mafi karancin albashin ma'aikata. Ta ce ta gamsu da shirin gwamnati.
Kungiyar kwadago reshen jihohi akalla shida sun sanar da janyewarsu daga yajin aikin da NLC za ta shiga a jihohin da ba a fara biyan sabon mafi karancin albashi ba.
Gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo ya amince a biya ma'aikatan jihar albashi na watan 13. Gwamnan ya kuma amince da daukar aiki ga wadanda suka kammala karatu.
Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya amince da sabon mafi karancin albashi ga ma'aikata. Gwamna Radda zai rika biyan albashin N70,000.
Gwamnatin jihar Osun ta sanar da cewa ma'aikata za su fara cin gajiyar sabon mafi karancin albashi na N75,000 daga ranar 1 ga watan Disamba, 2024.
Ministan Kwadago, Dingyadi, ya bayyana cewa gwamnati za ta hana shiga yajin aiki ta hanyar tattaunawa da 'yan kwadago da samar da hanyoyin warwarewar matsaloli.
Gwamnatin jihar Kaduna ta fara biyan sabon mafi karancin albashi na N72,000 ga ma'aikatan jihar a watan Nuwamba. Gwamnati na jiran koke daga ma'aikata.
Gwamantin Jigawa ta ayyana N70,000 a mafi ƙarancin albashi. Za a rika ba ma'aikata bashin suna noma tare da rage musu farashin kayan abinci a shaguna.
Albashin ma'aikata
Samu kari