Albashin ma'aikatan najeriya
Gwamnaan jihar Ebonyi, Francis Nwifuru, ya ba shugabannin kananan hukumomi wa'adi domin su biya ma'aikatan da ke karkashinsu hakkokin da suke bin bashi.
Gwamnatin jihar Oyo za ta fara biyan N80,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi daga Janairu 2025. Sabon tsarin zai fara daga Yulin 2024 kuma albashin watan 13 na nan.
Gwamna Umo Eno na jihar Akwa Ibom ya janye kansa daga yarjejejniyar da suka yi da kungiyar NLC kan albashi inda ya ce sai ya gama tantance ma'aikata.
Ma'aikatan Ebonyi za su dara. Gwamnansu, Francis Nwifuru zai gwangwajesu. Za a ba kowane ma'aikaci kyautar N150,000 don shagalin bikin kirismimeti.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi muhimman nade-nade. An ɗaga likkafar mutane akalla 23 a sassa 3 na jihar. Mutanen da aka naɗa sun ƙunshi limamai da malaman addini.
Kungiyoyi sun bayyana rashin jin dadin hukuncin mahukunta. Hukumomi a FCT sun nemi a fara biyan albashin 2025.NULGE ta ce za ta ci gaba da yajin aikin da ta ke yi.
CBN ya yi karin haske kan shirin ritayar ma'aikata 1000. Bankin ya musanta cewa shi ya tilasta masu ajiye aiki. Sannan ya fadi dalilin ware N50bn kudin sallama.
Gwamna Abdullahi Sule ya tabbatar da fara biyan sabon albashin N70,500, amma jihar ba za ta iya ɗaukar karin albashin da ake buƙata ba saboda rashin kuɗi.
Ma’aikatar kudi ta jihar Kwara ta ce biyan albashi yana gudana bisa tsarin rajistar KWSRRA, ma’aikatan da ba su samu albashin Nuwamba ba basu yi rijistar ba.
Albashin ma'aikatan najeriya
Samu kari