Albashin ma'aikatan najeriya
A labarin nan, za a ji cewa kasar Amurka ta fitar da wani rahoto da ke nuna yadda mafi karancin albashin Najeriya, N70,000 ya gaza sauya rayuwar talaka.
Kungiyar NLC ta bai wa gwamnati wa’adin kwanaki bakwai ta mayar da kudaden NSITF da ta karkatar, ta kuma gargaɗin shiga yajin aiki idan ba a dauki mataki ba.
Gwamna Bassey Otu na Cross River ya aiwatar da N70,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi ga ma’aikatan jihar, tare da shirin daga dajarar ma'aikatan wucin gadi.
A labarin nan, za a ji cewa gwamnatin tarayya ta fara biyan hakkokin ma'aikatan da ta rike na watanni biyu, yayin da ya rage na sauran watanni uku.
Ƙungiyar NUT a Kaduna ta ce malamain jihar za su tsunduma yajin aiki muddin gwamnati ta ƙi biyan albashi na N70,000 kamar yadda wasu jihohi suka fara.
Gwamnatin jihar Jigawa ta samu nasarar tsaftace bangaren ma'aikatanta. Gwamnatin ta gudanar da bincike inda ta gano dubunnan ma'aikata na bogi da ke karbar albashi.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince a biya ma'aikata da 'yan fansho kudade don su gudanar da bukukuwan babbar Sallah a cikin walwala da jindadi.
Gwamna Fintiri ya fara biyan sabon mafi karancin albashi na N70,000 ga ma'aikatan kananan hukumomin Adamawa. Ya ware ₦5bn don biyan hakkokin masu ritaya.
Ma’aikatan shari'a karkashin JUSUN sun rufe kotuna a Ibadan, a wani mataki na yajin aiki. Sun bukaci gwamnati ta kara masu albashi da alawus da 25% da 35%.
Albashin ma'aikatan najeriya
Samu kari