
Kananan hukumomin Najeriya







Wasu rahotanni sun ce ana hasashen batan tsohon shugaban karamar hukumar Kalgo a jihar Kebbi, Umar Namashaya Diggi bayan wani mummunan harin yan bindiga.

Babbar kotun Kano ta tabbatar da ƴancin kananan hukumomin jihar 44, ta ba ɗa umarnin ci gaba da sakar masu kuɗaɗensu kai tsaye ba tare da wata tangarɗa ba.

Jam'iyyar APC mai mulki a jihar Katsina ta lashe zaben shugabannin kananan hukumomin da aka gudanar a jihar. APC ta lashe dukkanin kujerun gabadaya.

Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya umarci shugabannin kananan hukumomi su fara biyan mafi karancin albashin N85,000 domin cika ka'idar aiki.

Shugaba Muhammadu Buhari ya ka da kuri'a a zaben kananan hukumomin jihar Katsina. Dandazon jama'a ne suka fito tarbar jama'a a lokacin da ya fito.

Rundunar 'yan sandan Katsina ta sanya dokar takaita zirga-zirga daga karfe 6 na safe zuwa 4 na yamma ranar Asabar. Wannan zai kawo zaman lafiya yayin zaben ciyamomi.

Korafe-korafe sun biyo bayan matakin Gwamna Umaru Bago na Niger ya nada tsohon shugaban APC, Jibrin Imam, a matsayin shugaban hukumar zaɓen jihar.

An yi ta ce-ce-ku-ce bayan gwamnatin jihar Ebonyi ta bukaci shugabannin kananan hukumomi 13 su dauki nauyin akalla Mahajjaci daya don aikin Hajjin 2025.

Babban Bankin Najeriya, CBN ya kawo wani tsari kan biyan kudin kananan hukumomi kai tsaye daga asusun Gwamnatin Tarayya da aka shirya tun watan Janairu.
Kananan hukumomin Najeriya
Samu kari