Labaran garkuwa da mutane
A labarin nan, za a ji cewa kotu ta fara zama a kan zargin wasu mutane uku da sace yara a Kano, sannan a yi safararsu zuwa jihar Delta domin sayar wa.
’Yan sanda sun hana ‘yan bindiga kai hari a dajin Byazhin, da ke birnin tarayya Abuja, sun kwato bindigar AK-47 da alburusai 30, sun kuma kara tsaurara tsaro a FCT.
A labarin nan nan, za a ji cewa shahararren mai garkuwa da mutanen nan, Kelvin Oniarah Ezigbe, da ya sace fitaccen lauya, Mike Mike Ozekhome (SAN) ya samu sassauci.
Rundunar Yan Sandan Kano ta kama wani matashi dan shekara 27 da ake kira Yello bisa zargin hannu a aatar basarake da masa fashi tun shekarar 2023.
Jami'an tsaro sun samu nasarar hallaka wani tantirin dan ta'adda a jihar Kwara. Dan ta'addan ya kware wajen yin garkuwa da mutane don neman kudin fansa.
Rundunar ’yan sanda a Bauchi ta ceci mutane biyu da aka sace a Alkaleri, ta kuma cafke mutum uku da ake zargi da garkuwa yayin da ake ci gaba da neman sauran miyagu.
Rundunar yan sanda reshen Zamfara ta ce yan bindiga sun fara daukar salom kai hari masallaci ne saboda su ja hankalin jama'a bayan ganin abin da ya faru a Katsina.
Wasu miyagun yan bindiga da ba a san manufarsu ba sun yi awon gaba da matar fasto a yankin karamar hukumar Obi da ke jihar Nasarawa, sun hada da wata bakuwa.
Wasu da ake zargi 'yan bindiga masu garkuwa da mutane ne sun sace wani mutum a karamar hukumar Dukku sun kashe shi bayan karbar kudin fansa Naira miliyan 5.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari