Yan bindiga
Ƴan bindiga sun sace mutum biyu a yankin Mpape na birnin tarayya Abuja cikin tsakar dare. Jami'an ƴan sanda sun ceto mutanen bayan fafatawa da ƴan bindigan.
Jami'an yan sanda a jihar Bauchi sun yi nasarar damke wasu masu garkuwa da mutane bakwai sannan sun kuma kwato makamai guda hudu a karamar hukumar Alkaleri.
Dakarun sojoji a jihar Zamfara sun fattaki ƴan bindiga tare da ceto wasu mutum tara da suka yi garkuwa da su a ƙauyen Mailere cikin ƙaramar hukumar Bukkuyum.
Wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi ajalin wani dan kasuwa mai suna Chinonso Ugwu a kauyen Balele da ke karamar hukumar Ningi a jihar Bauchi.
Rundunar sojin Najeriya da ke karamar hukumar Mangu a jihar Plateau ta hallaka tsagera 'yan bindiga uku da kwato muggan makamai a hannunsu bayan wani artabu.
Shugaban jam'iyyar APC na jihar Ekiti da aka sace ya kubuta daga hannun ƴan bindiga. Jami'an tsaro ne suka ceto shugaban na APC da wasu mutum biyu da aka sace.
Dakarun sojoji na atisayen 'Operation Safe Haven' sun yi arangama da miyagun ƴan bindiga a jihar Plateau. Sojojin sun halaka ƴan bindiga uku da kwato makamai.
Babban hafsan sojin Najeriya, Manjo Janar Taoreed Lagbaja ya bukaci gwamnonin Arewa maso Yamma su cire hannunsu a harkar 'yan bindiga don ba su daman dakile su.
Gwamnan jihar Benue, Rabaran Hyacinth Alia ya bayyana haƙiƙanin masu aikata kashe-kashe a jihar. Ya bayyana cewa ƴan cikin gida ne ba baƙi ba ke aikata hakan.
Yan bindiga
Samu kari