Yan bindiga
An shiga fargaba bayan 'yan bindiga sun yi garkuwa da fitaccen Fasto kuma shugaban cocin RCCG a jihar Oyo da sauran fasinjoji a mota a kan hanyarsu ta zuwa Legas.
Wasu 'yan bindiga sun hallaka akalla sojoji shida a jihar Neja tare da yin garkuwa da wani Kyaftin a wani mummunan hari a daren Juma'a 19 ga watan Afrilu.
An samu asarar rayuka bayan an gwabza fada a tsakanin 'yan bindiga da 'yan banga a jihar Sokoto. Mutane da dama sun rasa rayukansu a dalilin arangamar.
A yayin da jami'ar jihar Filato ta sanar da rufe makarantar na kwanaki 10, gwamnan jihar Mutfwang ya yi Allah-wadai kan harin da aka kai jami'ar da ke Bakkos.
Gwamna Usman Ododo na jihar Kogi ya nemi alfarmar Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan matsalolin rashin tsaro da ambaliyar ruwa da suka addabi jihar da kewayenta.
Mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu ya bayyana dalilan da suka haddasa matsalar rashin tsaron da ake fama da ita a Najeriya.
Wani luguden wuta da aka yi ya hallaka mutane da-dama a wani kauye da ke jihar Zamfara. Hakimin Dogan Daji a Muradun ya ce mutanensu aka kashe ba 'yan bindiga ba.
Wasu miyagun ƴna bindiga sun halaka mutane akalla 20 a kauywn Anguwar Danko da ke yankin ƙaramar hukumar Birnin Gwari a jihar Kaduna ranar Laraba.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun aikata ta'asa a kan titin Kakangi zuwa Birnin Gwari. Tantiran sun hallaka jami'an tsaro na 'yan banga mutum 3 tare da sace 'yan kasuwa.
Yan bindiga
Samu kari