Jihar Edo
Gwamnonin Arewa karkashin jagorancin Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya sun yi Allah-wadai da kisan matafiya a Edo, suna cewa wannan abin takaici ne da ya sabawa doka.
Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar ya bukaci hukumomin tsaro su gudanar da bincike na adalci kuma a bayyane kan kisan ƴan Arewa a Edo.
Jagoran NNPP na kasa, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya yi Allah wadai da kisan matafiya ƴan Arewa da aka ce suna hanyar zuwa Kano a jihar Edo, ya nemi a ɗauki mataki.
Gwamna Monday Okpebholo ya yi Allah wadai da kisan ƴan Arewa a garin Uromo na jihar Edo, ya ba da umarnin gudanar da bincike don hukunta mau hannu.
Fitaccen mai sharhi, Reno Omokri, ya soki kisan wasu matafiya da ake zargin suna kan hanyarsu daga Port Harcourt zuwa Kano don hutun bukukuwan Sallah.
Wasu mutanen Arewa da suka fito daga Fatakwal zuwa Kano sun hadu da tsautsayi a jihar Edo. An kona yan Arewa 16 a Edo suna dawowa gida hutun sallar azumi.
Gwamna Monday Okpebholo ya bayyana cikakken goyon bayansa kan ayyana dokar ta ɓaci a jihar Ribas, ya tsame kansa daga matsayar gwamnonin Kudu maso Kudu.
Gwamna Monday Okpebholo na jihar Edo ya sha alwashin ba Bola Tinubu kuri'u a 2027 yayin da ya karɓi shugabannin kananan hukumomi 17 da suka sauya sheka zuwa APC.
Jam'iyyar APC ta zama mai rinjaye a Majalisar Dokokin jihar Edo yayin da ƴan Majalisa huɗu daga PDP da LP suka tattara kayansu suka kƙma cikinta.
Jihar Edo
Samu kari