Kotun Kostamare
Mai martaba sarki na masarautar Orile Ifo, Oba Abdulsemiu Ogunjobi ya tsinci kansa a gidan gyaran hali bayan gaza cika sharuddan belin da aka ba shi a Ogun.
Wani magidanci, Yahaya ya roƙi wata kotun yanki a Abuja ta raba aurensa da mai ɗakinsa, ya ce tun da ya musulunta zaman lafiya ya bar gidansa da matarsa.
Kwamishina a jihar Bauchi, Abdulrazak Nuhu Zaki, ya yi martani kan zargin satar yarinya, yana mai cewa Zainab diyarsa ce ta jini kuma yana da hakki a kanta.
Mai shari'a Olatunji Oladunmoye na kotun Gwagwalada ya tsare Nazifi da Bilkisu kan laifin zina. Bilkisu ta ce Nazifi bai san tana da aure ba inda ta roki sassauci.
Babbar kotun majistare da ke sauraron shari'ar tsohon jami'in gwamnatin jihar Kaduna, Muhammad Bashir Sa'idu ta haba belinsa biyo bayan tuhumarsa da almundahana,
Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta samu Cikas a rusau da ta yi. Babbar kotun jiha ta nemi a biya diyyar biliyoyin Naira ga kamfanin Lamash properties.
Tsohon gwamnan Kogi, Yahaya Bello zai sake nufar Kogi. A wannan karon, shi ne zai shigar da kara. Ya zargi wata jarida da son hada shi fada da shugaba Bola Tinubu.
Gwamnatin tarayya ta zargi Facebook da sabawa ka'idoji don haka aka ci ta tara. A yanzu alkali ya bukaci hukumar ARCON ta bar magaar wannan haraji na N60bn.
Wata mata a Kaduna ta gurfana gaban kotu kan kashe diyarta da guba. Kotun ta umarci NSCDC ta tura fayil zuwa daraktan shari’a don shawara kan karar.
Kotun Kostamare
Samu kari