
Mafi karancin albashi







Gwamnan jihar Ekiti, Dr. Biodun Oyebanji ya amince da N70,000 a matsayin sabon mafi ƙarancin albashin ma'aikatan gwamnati, ya ce har ƴan fansho za su ga canji.

Ministan Abuja, Nyesom Wike ya amince da biyan N70,000 ga ma'aikatan birnin Tarayya Abuja domin ragewa ma'aikatan halin tsadar rayuwa da ake ciki a Najeriya.

Gwamnan Benue ya yi karin mafi ƙarancin albashi zuwa N75,000 ga ma'aikata. Gwamnan ya ce ya kara albashi sama da yadda Tinubu ke biya a matakin tarayya.

Gwamna Umo Eno na jihar Akwa Ibom ya yi magana kan dalilin jinkiri da aka samu kan fara biyan mafi ƙarancin albashi inda ya ce sai an gama tantance su.

Gwamnan jihar Plateau ya amince da sabon mafi karancin albashi ga ma'aikatan jihar. Caleb Mutfwang ya amince a fara biyan ma'aikata sabon albashin N70,000.

Gwamnatin jihar Zamfara karkashin jagorancin Gwamna Dauda Lawal ta bayyana cewa nan ba da jimawa ba za ta fara biyan sabon mafi karancin albashi na N70,000.

Shugabannin ƙungiyar kwadago sun soki jihohin da ke jan kafa kan albashin N70,000, suna ganin hakan take hakkin ma’aikata ne a wannan mawuyacin lokaci.

Gwamnan jihar Taraba, Agbu Kefas, ya amince da sabon mafi karancin albashi ga ma'aikatan jihar. Gwamnan zai fara biyan sabon albashin daga watan Nuwamba.

Fasto Umo Eno, gwamnan jihar Akwa Ibom ya ba da tabbacin cewa zai biya ma’aikatan jihar albashi biyu a watan Disamba domin inganta bukukuwan Kirsimeti.
Mafi karancin albashi
Samu kari