Jerin Abubuwa 2 da Aka Ƙulla da Nufin Wargaza Shirin Tazarcen Bola Tinubu a 2027

Jerin Abubuwa 2 da Aka Ƙulla da Nufin Wargaza Shirin Tazarcen Bola Tinubu a 2027

  • Shugaban kwamitin rikon kwarya na APC a jihar Ribas, Tony Okocha ya yi zargin cewa wasu na yunkurin karɓe jam'iyyar a jihar
  • Okocha ya bayyan acewa hakan na ɗaya daga cikin makircin da aka fara kitsawa domin hana Bola Tinubu tazarce a zaɓen 2027
  • Jam'iyyar APC mai adawa a jihar Ribs ta kara shiga cikin rigima biyo bayan hukuncin babbar kotun jiha na rusa kwamitin Okocha

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Rivers - shugaban riko na APC a jihar Ribas, Tony Okocha ya ce hukuncin kotu na rusa kwamitin da yake jagoranta wata manaƙisa ce da aka ƙulla da nufin karɓe jam'iyyar.

Mista Okocha ya bayyana cewa rigingimun da suka ɓarke a APC ta jihar Ribas na ɗaya daga cikin abubuwan da aka shirya domin daƙile tazarcen Bola Ahmed Tinubu a 2027.

Kara karanta wannan

Malami ya faɗi wanda zai lashe zaben shugaban ƙasa idan PDP ta fito da Atiku a 2027

Shugaban Kasa Bola Tinubu
Jigon APC ya jero abubuwa 2 da za su kawo tarnaki a tazarcen Tinubu a 2023 Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

Rikicin APC: Okocha ya aikawa Tinubu saƙo

Kamar yadda The Nation ta tattaro, shugaban APC na rikon kwarya a Rivers ya ce kotun ba ta da hurumin tsoma baki a harkokin cikin gida na jam'iyyar siyasa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sakamakon haka Tony Okocha ya ce ba ruwan kotu da batun shugabancin jam'iyyar.

Da yake jawabi ga ƴan jarida a Abuja, Mista Okocha ya nanata cewa APC ta jima da dakatar da Emeka Bike (wanda ke tutiyar shi ne shugaban APC) da wani Barista Iheanyichukwu Dike.

Tony Okocha ya ce:

"Mu na kotu a matsayinmu na ƴan ƙasa masu bin doka, a wurin mu hukunci ko daga banɗaki ya fito za mu yi biyayya, amma yanzu dai mun shigar da bukatar dakatar da hukuncin a kotun ɗaukaka ƙara.
"Tun da jimawa kotun ƙoli ta raba gardama, ta yanke cewa bai kamata kotuna su riƙa sa baki a harkokin cikin gida na jam'iyyu ba. Zaɓen shugaban jam'iyya lamari ne na cikin gida."

Kara karanta wannan

Ana fargabar kitsa makarkashiya ga shirin tazarcen shugaba Tinubu a zaben 2027

Abubuwa 2 da Okocha ya ambata

1. Hukuncin rusa kwamitin rikon kwarya na APC a Rivers

2. Rigingimun da wasu suka jawo a APC.

Farfesa Falola ya magantu kan zanga-zanga

A wani rahoton kuma Farfesa Toyin Falola na jam'iar Texas ya yi magana kan zanga-zangar nuna adawa da halin ƙuncin da aka yi a ƙasar nan.

Farfesan ya bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu bai magance matsalolin da suka sanya mutane suka fito kan tituna.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262