Malami Ya Faɗi Wanda Zai Lashe Zaben Shugaban Kasa Idan PDP Ta Fito da Atiku a 2027

Malami Ya Faɗi Wanda Zai Lashe Zaben Shugaban Kasa Idan PDP Ta Fito da Atiku a 2027

  • Primate Elijah Babatunde Ayodele ya bayyana cewa jam'iyyar PDP za ta sha kaye matukar ta sake ba Atiku Abubakar tikitin takara a 2027
  • A wani faifan bidiyo da ya fitar, babban malamin ya ce Atiku ba zai iya jan ragamar PDP zuwa nasara ba a zaɓen shugaban kasa na gaba
  • Wazirin Adamawa ya riƙe kujerar mataimakin shugaban kasa daga 1999 zuwa 2007 kuma ya nemi takara sau da dama bai samu nasara ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Babban limamin cocin evangelical, Primate Elijah Babatunde Ayodele ya yi hasashen cewa PDP ta mutu murus idan ta sake tsaida Atiku Abubakar takara a zaɓen 2027.

Fitaccen limamin kirista ya ce cikin sauƙi APC za ta buga PDP da kasa idan har jam'iyyar adawa ta sake miƙawa Atiku tikitin takarar shugaban ƙasa.

Kara karanta wannan

Sabon ɗan Majalisar PDP da aka rantsar ya yi magana kan yiwuwar sauya sheka

Primate Ayodele.
Primate Ayidele ya hango karshen PDP idan ta sake ba Atiku Abubakar takara a 2027 Hoto: Ayodele
Asali: Facebook

Primate Ayodele ya bayyana haka ne a wani faifan bidiyo da ya wallafa a shafinsa na manhajar X wanda aka fi sani da Twitter ranar Alhamis, 15 ga watan Agusta.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tarihin takarar Atiku Abubakar

Legit Hausa ta tattaro cewa Atiku, wazirin Adamawa ya nemi zama shugaban ƙasa sau da dama amma Allah bai ba shi nasara ba.

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya nemi ya tsaya takarar kujera lamba ɗaya a Najeriya a 1993, 2007, 2011, 2015, 2019, da kuma 2023.

Ayodele ya yi hasashen takarar Atiku

Limamin cocin ya bayyana cewa idan har Atiku ya lashe tikitin PDP, to jam'iyyar ba za ta kai labari ba.

Ayodele ya ce:

"PDP ku karkaɗe kunnenku da kyau, idan kuna son shan kaye, to ku ba Atiku tikitin takarar shugaban ƙasa, za ku ga yadda za a yi ƙasa-ƙasa da ku, cikin sauki APC za ta samu nasara.

Kara karanta wannan

Jihar Kudu ta nemi daukin shugaban APC Ganduje domin ceto siyasar Tinubu a 2027

"Atiku ba shi ne mafitar PDP a 2027 ba, idan kuka sake gwada shi, to ku tabbaci haƙiƙa a siyasa PDP ta mutu, ajalin PDP kenan,"

Legas: An maka gwamna a kotu kan rusau

A wani rahoton na daban, an ji wata shugabar makaranta Paulin Eboagwu da mai gidanta sun kai ƙarar gwamnan Legas, Babajide Sanwo-Olu a kotu.

Masu karar sun roki babbar kotun jihar Legas ta umarci waɗanda ake tuhuma su biya diyyar N11bn kan rusa ɓangaren makarantarsu ba bisa ƙa'ida ba.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262