Babbar Kotu Ta Jikawa Ganduje Aiki, Ta Tsige Shugaban APC da Wasu Ƙusoshin Jiha

Babbar Kotu Ta Jikawa Ganduje Aiki, Ta Tsige Shugaban APC da Wasu Ƙusoshin Jiha

  • Kotu ta sauke muƙaddashin shugaban jam'iyyar APC na jihar Ribas, Cif Tony Okocha, ta dawo da Emeka Beke kan muƙaminsa
  • Mai shari'a Sika Aprioku ya ce APC ba ta da hurumin korar zaɓaɓɓun shugabanninta na jiha tare da naɗa kwamitin rikon ƙwarya
  • Tuni dai kwamitin riƙon kwaryar APC na jihar Ribas ya yi watsi da wannan hukuncin, ya sha alwashin ɗaukaka ƙara

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Rivers - Babbar kotun jiha mai zama a Fatakwal ta ta soke matakin tsige zaɓaɓɓun shugabannin APC na jihar Ribas karkashin jagorancin Emeka Beke.

Mai shari'a Sika Aprioku na babbar kotun ne ya yanke wannan hukuncin a ranar Litinin, 12 ga watan Agusta, 2024.

Kara karanta wannan

Atiku ya caccaki Tinubu, ya bayyana inda gwamnatinsa ta samu matsala

Abdullahi Ganduje.
Kotu ta rushe kwamitin riƙon kwarya na APC a jihar Rivers Hoto: Dr. Abdullahi Umar Ganduje
Asali: Twitter

Aƙalin ya yanke hukuncin cewa kwamitin ayyuka na jam’iyyar APC ta kasa ya tafka kuskure da ya rusa zaɓaɓɓun shugabanni na jihar Ribas karkashin Emeka haka kurum.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kar yadda jaridar Punch ta tattaro, mai shari’a Aprioku ya bayyana cewa jam’iyyar APC ta ƙasa ba ta da hurumin korar zababbun shugabanni na kowace jiha.

Kotu ta sauke Okocha daga kujerar APC

Haka nan kuma kotu ta ce APC ba ta da ikon naɗa wani kwamitin rikon kwarya gabanin ƙarewar wa'adin zaɓaɓɓun shugabannin jam'iyya.

Sakamakon haka ne kotun ta tsige shugaban APC na rikon ƙwarya na Ribas, Chief Tony Okocha tare da dukkan mambobin kwamitinsa, sannan ta mayar da Emeka.

Mai shari’a Aprioku ya kuma haramtawa Tony Okocha da mambobin CTC ci gaba da ayyana kansu a matsayin shugabannin jam’iyyar APC a jihar Ribas.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Babban jigo ya faɗi dalili 1 da ya kamata a tsige Tinubu da wasu gwamnoni

Jam'iyyar APC za ta ɗaukaka ƙara

Hukuncin ya biyo bayan karar da Sam Etetegung ya shigar yana ƙalubalantar Abdulahi Ganduje, shugaban APC na kasa da kwamitin CTC.

Kwamitin riko kwarya na APC a jihar karkashin jagorancin Cif Tony Okocha, ya yi watsi da hukuncin da babbar kotun jihar Ribas ta yanke ranar Litinin.

Mai magana da yawun CTC, Chibike Ikenga, ya ce tuni jam'iyyar ta umarci tawagar lauyoyinta su ɗaukaka ƙara zuwa gaba, rahoton Vanguard.

APC ta fara shirin dawo da Ndume

A wani rahoton kuma jam'iyyar APC ta sake magana kan yiwuwar dawo da Sanata Ali Ndume mukaminsa na mai tsawatarwa a majalisa.

APC ta tabbatar da cewa ta fara magana da shugabannin majalisar dattawa kan dawo da Sanata Ali Ndume kan matsayinsa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262