Lagas, Delta: Jerin Jihohin Da Peter Obi Ya Lashe a Zaben Shugaban Kasa Na 2023

Lagas, Delta: Jerin Jihohin Da Peter Obi Ya Lashe a Zaben Shugaban Kasa Na 2023

Hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta (INEC) ta kammala tattara sakamakon zaben shugaban kasa na 2023.

An tattara sakamakon zaben na kasa a cibiyar taro na kasa da kasa da ke Abuja karkashin jagorancin Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu.

Peter Obi yana kada kuri'a
Lagas, Delta: Jerin Jihohin Da Peter Obi Ya Lashe a Zaben Shugaban Kasa Na 2023 Hoto: @PeterObi
Asali: Twitter

Zaben shugaban kasa na 2023: Tattara sakamako na kasa a Abuja

An tattara sakamakon jihohi 36 harda babban birnin tarayya a matakin kasa a Abuja. Sune:

  1. Jihar Ekiti
  2. Jihar Kwara
  3. Jihar Osun
  4. Jihar Ondo
  5. Jihar Ogun
  6. Jihar Oyo
  7. Jihar Yobe
  8. Jihar Enugu
  9. Jihar Lagos
  10. Jihar Gombe
  11. Jihar Jigawa
  12. Jihar Adamawa
  13. Jihar Katsina
  14. Jihar Nasarawa
  15. Jihar Niger
  16. Jihar Benue
  17. FCT
  18. Jihar Akwa Ibom
  19. Jihar Edo
  20. Jihar Abia
  21. Jihar Kogi
  22. Jihar Bauchi
  23. Jihar Plateau
  24. Jihar Bayelsa
  25. Jihar Kaduna
  26. Jihar Kebbi
  27. Jihar Zamfara
  28. Jihar Kano
  29. Jihar Sokoto
  30. Jihar Cross River
  31. Jihar Delta
  32. Jihar Ebonyi
  33. Jihar Anambra
  34. Jihar Taraba
  35. Jihar Borno
  36. Jihar Rivers
  37. Jihar Imo

Kara karanta wannan

Zaben Shugaban Kasa: Peter Obi Ya Lallasa Atiku Da Tinubu a Jihar Cross River

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Daga cikin jihohin 36 da birnin tarayya da aka lissafa a sama, dan takarar jam'iyyar All Progressives Congress (APC) Bola Tinubu ya lashe 12 yayin da dan takarar jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Atiku Abubakar, shima ya lashe 12.

Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour Party (LP) shima ya lashe 12 yayin da Rabiu Kwankwaso na New Nigeria Peoples Party (NNPP) ya lashe jiha daya: Kano.

Zaben shugaban kasar 2023: Jihohi nawa Peter Obi ya lashe:

Zuwa yanzu, Peter Obi ya lashe jihohin da ke kasa bayan tattara sakamako a matakin kasa:

  1. Jihar Lagos
  2. Jihar Enugu
  3. Jihar Nasarawa
  4. Jihar Ebonyi
  5. Jihar Abia
  6. Jihar Delta
  7. Jihar Anambra
  8. Jihar Plateau
  9. FCT
  10. Jihar Edo
  11. Jihar Cross River
  12. Jihar Imo

Bola Tinubu ya lashe zaben shugaban kasa, INEC

Kara karanta wannan

Sakamakon Zabe: An Yi Wa Atiku Kayen Raba Ni da Yaro a Jihar Abokin Takararsa Okowa

A gefe guda, mun ji cewa hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta, INEC, ta ayyana dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa.

Tinubu ya yi nasara ne bayan ya lashe kuri'u mafi rinjaye a babban zaben kasar da ya gudana a fadin jihohi 36 harda babban birnin tarayya Abuja a ranar Asabar, 25 ga watan Fabrairun 2023.

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng

Tags:
Online view pixel