Tsohon Gwamna Ya Ci Amanar APC, Yana Tallata ‘Dan Takarar Jam’iyyar Adawa Karara

Tsohon Gwamna Ya Ci Amanar APC, Yana Tallata ‘Dan Takarar Jam’iyyar Adawa Karara

  • Ibikunle Amosun ya dage sai an hana Dapo Abiodun zarcewa a matsayin Gwamnan jihar Ogun
  • Yadda ya yake shi a 2019, ‘Dan siyasar ya dage dole sai an yi waje da Gwamna Abiodun a zaben 2023
  • A cewar Amosun murdiya aka yi har APC ta iya lashe zaben da aka yi a lokacin da zai bar karagar mulki

Ogun - Ibikunle Amosun wanda Sanata a karkashin Jam’iyyar APC, ya halarci taron ‘dan takarar ADC a zaben Gwamnan jihar Ogun a zaben bana.

Daily Trust ta kawo rahoto a ranar Laraba cewa Ibikunle Amosun bai tare da Dapo Abiodun.

A maimakon a ga Sanata Ibikunle Amosun yana taya Gwamna Dapo Abiodun yakin neman zaben tazarce, sai ga shi yana goyon bayan 'yan adawa.

Dapo Abiodun ne ya gaji Ibikunle Amosun a Mayun 2023 a karkashin jam’iyyar APC da ya yi mulki, amma babu jituwa tsakaninsa da magajin shi.

Kara karanta wannan

Miyagu Sun Sace Darektan Yakin Neman Zaben Jam’iyyar APC a Wajen Yawon Kamfe

Kasa Otegbeye, Sama Tinubu

A zaben Gwamna da za ayi a watan Maris, tsohon Gwamnan na Ogun zai goyi bayan Biyi Otegbeye na ADC ya doke jam’iyya mai mulki watau APC.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Amma a zaben shugaban kasa, Sanatan na Ogun ta tsakiya yana cikin wadanda ke goyon bayan Bola Ahmed Tinubu ya karbi shugabancin Najeriya.

Ibikunle Amosun
Sanata Ibikunle Amosun a taron ADC Hoto: dailypost.ng
Asali: UGC

Amosun zai yi wake da shinkafa

Amosun ya janye neman takarar shugaban kasarsa, ya goyi bayan Bola Tinubu a zaben fitar da gwani, amma a gida bai tare da ‘dan takaransu na APC.

Daily Post ta ce kwatsam aka ga ‘Dan majalisar a wajen taron kaddamar da yakin neman zaben Gwamna na ADC a fadar Ake da ke birnin Abeokuta.

Rahoton ya ce an ga shi yau da karfe 1:49 wajen gangamin da ‘yan jam’iyyar ADC suka shirya.

Kara karanta wannan

Ta Rikice Wa Atiku, Gwamna Wike Ya Tuna Baya, Ya Faɗi Hukuncin da Zasu Yanke Wa PDP a Zaben 2023

Zuwan Amosun wanda ya yi Gwamna sau biyu a Ogun ya farantawa mabiyansa da ‘yan jam’iyyar hamayya ta ADC rai a wajen yawon kamfen da ake yi.

Leadership ta ce tsohon Gwamnan ya soki Gwamnati mai-ci, sannan ya jagoranci tawaga zuwa fadar Mai martaba Sarkin Egba, Adedotun Gbadebo.

Ya APC za ta yi da Ibikunle Amosun?

Tun a baya an ji labari Ibikunle Amosun wanda ya yi mulki tsakanin 2011 zuwa 2019 ba zai marawa magajinsa da ke takara jam’iyyarsa baya a zabe ba.

A zaben da ya wuce, Sanata Amosun ya goyi bayan Adekunle Akinlade na APM, daga baya sai aka ji ‘dan siyasar ya sauya-sheka zuwa jam’iyyar PDP.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng