Biyubabu: Lawan Da Akpabio Ba Sa Cikin Yan Takarar Senata, INEC

Biyubabu: Lawan Da Akpabio Ba Sa Cikin Yan Takarar Senata, INEC

  • Hukumar Zabe INEC ta ce ba ta amince da saka sunan Sanata Ahmed Lawan da Godswill Akpabio a matsayin yan takarar senata a yankunan su ba
  • Hukumar INEC ta ce zata yi amfani da kwafin fom din sunaye yan takara da jam'iyyu suka gabatar mata kafin ta rufe dandalin tantance sunaye
  • Form EC9 shine fom din sunayen yan takara da jam’iyyun siyasa ta mika wa INEC kuma sune a tashar INEC

Abuja - Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta ce ba ta amince da saka sunan Sanata Ahmed Lawan matsayin ‘yan takarar senata a Yobe ta Arewa da Godswill Akpabio a matsayin dan takarar senata a Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma ba. Rahoton LEADERSHIP

Kara karanta wannan

Rikicin Atiku da Wike: Jam'iyyar PDP ta dage zaman NEC saboda ta'azzarar rikicin gida

Hukumar INEC ta ce bata dauki daya daga cikin mutanen biyu a matsayin yan takarar Sanata a zaben 2023 mai zuwa ba.

Kwamishinan INEC na kasa kuma shugaban kwamitin yada labarai da wayar da kan masu kada kuri’a, Festus Okoye, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata mai taken: ‘zarge-zarge dangane da tantance ‘yan takara a wasu gundumomin sanatoci da aka gabatar wa ‘yan jarida.

Lawan
2023 : Lawan Da Akpabio Ba Sa Cikin Yan Takarar Senata INEC FOTO PremiumTIMES
Source: UGC

Okoye ya ce a matsayin shaida na rawar da Hukumar ta taka, tun da farko an gabatar da kwafin gaskiya na Form 9C da jam’iyyun suka shigar kuma Hukumar ta samu a ranar 17 ga Yuni, 2022 lokacin da aka rufe dandalin tantance sunaye.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Domin a fayyace, ya ce Form EC9 shine fom din sunayen yan takara da jam’iyyun siyasa ta mika wa INEC kuma sune a tashar ta INEC.

Ya ce an yi nuni a fili a kan sunan fom din da aka karba a ranar 17 ga watan Yuni, 2022 lokacin da aka rufe tashar.

Kara karanta wannan

Tinubu Zai Fuskanci Matsala Tun Yanzu, Ana Hure Kunnen Darektan Kamfen da Ya Zaba

Dalibin Makarantar Sakandare Ya Kera Na'urar Mutum Mutumi Da Kansa A Jihar Kano

A wani labari kuma, Isah Barde, matashi dan shekara 17 da ya kammala karatunsa na sakandare a jihar Kano, ya kera Na'urar Mutum Mutumi daga tarkace, inda ya yi amfani da kwali, bututu, ledodi, moto, aluminum, da dai sauransu, a matsayin kayan aikin sa. rahoton Daily Trust

Isah yayi nazarin karantar fasahar kere-kere da zama kwararre a harkar leken asiri, duk da matsalar kudi da ke gabansa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Tofa avatar

Ibrahim Tofa