Da dumi: Dan takarar jam'iyyar SDP, Segun Oni, ya lashe akwatin zaben rumfarsa

Da dumi: Dan takarar jam'iyyar SDP, Segun Oni, ya lashe akwatin zaben rumfarsa

Dan takarar kujerar gwamnan jihar Ekiti, Segun Oni, ya lashe akwatin zaben rumfarsa dake karamar hukumar Ido-Osi.

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Segun Oni na cikin yan takara uku wadanda ke taka rawar gani wajen zaben, musamman bisa sakamakon da suka fito kawo yanzu.

Oni, wanda ya taba Gwamnan jihar kafin kotu ta tsigesa kuma Gwamna Fayemi ya dane kan mulki.

Bayan fadi a zaben fidda gwnain APC, Segun Oni ya sauya sheka jam'iyyar SDP don takara.

Ya kada kuri'arsa a rumfar zaben PU6, gunduma ta 4, Ogbon Iro, Ifaki-Ekiti, karamar hukumar Ido-Osi

SDP -218

APC -15

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

APP -3

PDP -2

NNPP - 2

Segun Oni
Da dumi: Dan takarar jam'iyyar SDP, Segun Oni, ya lashe akwatin zaben rumfarsa
Asali: Facebook

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng