Wani na kusa da Buhari, ya shiga sahun masu neman yin takarar Shugaban kasa a APC

Wani na kusa da Buhari, ya shiga sahun masu neman yin takarar Shugaban kasa a APC

  • Babu mamaki nan da ‘yan kwanaki kadan a ji labarin Ikeobasi Mokelu ya yanki fam a jam'iyyar APC
  • Tsohon shugaban kungiyar ‘I Stand With Buhari’, na kasa, Cif Ikeobasi Mokelu ya na neman takara
  • Mokelu ya na tare da Shugaban kasa, kuma sun rike mukami tare da shi a gwamnatin Sani Abacha

Anambra – Labari na zuwa cewa Ikeobasi Mokelu ya na niyyar yin takarar shugaban kasa a Najeriya, kuma zai tsaya ne a karkashin jam’iyyar APC.

Jaridar Punch ta ce Cif Ikeobasi Mokelu ya kammala shirye-shiryen tsaf na sayen fam din neman tikitin shugaban kasa a jam’iyyar APC mai mulki a kasa.

Ikeobasi Mokelu ya na cikin kusoshin jam’iyyar APC a kudancin Najeriya, sannan ana ganin ya na cikin na-kusa da shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Idan rahoton da mu ka samu ya tabbata, za a ji Mokelu nan da ba da dadewa ba, ya lale makudan kudi domin sayen fam din shiga takarar shugaban kasa a APC.

Kara karanta wannan

Masu fasa bututu sun taso Najeriya a gaba, ana asarar Naira Biliyan 600 a kowace rana

Ana tunanin tsohon Ministan ya na tare da wasu masu rike da madafan iko a fadar shugaban kasa.

Alakar Mokelu da Buhari

Gabanin zaben 2019, a shekarar 2018 ne Mokelu ya kirkiro tafiyar nan ta ‘I Stand With Buhari’, kuma ya na cikin masu kai wa da komawa a fadar Aso Villa.

'Ya 'yan APC
Wasu magoya bayan Jam'iyyar APC Hoto: dailypost.ng
Asali: UGC

Yayin da Muhammadu Buhari ya shugabanci hukumar PTF a lokacin Janar Sani Abacha, Mokelu shi ne Ministan harkokin yada labarai a gwamnatin sojan.

Siyasar APC a jihar Anambra

Kafin nan, Cif Mokelu zai zauna da ‘ya ‘yan jam’iyyar APC a mazabarsa ta Ubolo Unodu da ke garin Oraifite, a karamar hukumar Ekwusigo a jihar Anambra.

Sannan ‘dan siyasar zai tattauna da manyan jam’iyyar APC daga yankin kudu maso gabashin Najeriya domin shaida masu burinsa na neman shugabanci.

Kara karanta wannan

Dokubo Asari ya caccaki Gwamnan PDP, ya ce takararsa a 2023 ba za ta kai labari ba

Tun a jiharsa ta Anambra, Mokelu zai iya samun cikas a APC domin akwai masu zuga tsohon Gwamna, Chris Ngige ya fito takara a karkashin jam’iyyar.

Yanzu haka Sanata Chris Ngige ya na cikin manyan Ministoci a gwamnatin Muhammadu Buhari.

Arewa sun ci rabonsu – Bode George

A gefe guda kuma, an ji cewa Olabode George ya sanar da shugaban PDP na kasa cewa ba zai yiwu a iya cin zabe yayin da ake fada a Jihohin Legas da Kano ba.

Sannan tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar ya hakikance a kan dole wanda zai zama shugaban kasa ya fito daga kudancin Najeriya a zaben 2023.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng