Masu fasa bututu sun taso Najeriya a gaba, ana asarar Naira Biliyan 600 a kowace rana

Masu fasa bututu sun taso Najeriya a gaba, ana asarar Naira Biliyan 600 a kowace rana

  • Shugaban kamfanin man NNPC, Mele Kolo Kyari ya bayyana a gaban majalisar wakilan tarayya
  • Mele Kolo Kyari ya yi tir da aikin masu fasa bututun danyen mai da masu matatan da ba su da rajista
  • Wannan matsala ta jawo ake tunanin gwamnatin tarayya ta yi asarar $1.5bn a cikin farkon 2022

Abuja - Shugaban kamfanin mai na kasa watau NNPC, Mele Kolo Kyari ya koka a game da yadda ‘yan fasa kauri suke cin karensu babu babbaka a yau.

Daily Trust ta rahoto Mele Kolo Kyari ya na cewa ana samun matsaloli a dalilin dayen aikin masu fasa bututu da kuma masu matatan da ba a san da su ba.

Mele Kyari ya yi wannan bayani ne a sa’ilin da ya bayyana a gaban kwamitin harkar mai na majalisar wakilan tarayya a ranar Talatar da ta gabata.

Kara karanta wannan

Dattijon arewa ya yi fallasa, ya sanar da abinda Gumi ya fadi wa 'yan bindigan daji

Shugaban kafmfanin NNPC ya shaidawa ‘yan majalisa cewa aikin mabarnatan ya jawo an rasa danyen man Dala biliyan 1.5 daga Junairu zuwa yau.

A cewar Kyari, tattalin arzikin kasa ya yi baya a sanadiyyar karancin man da ake hakowa saboda masu fasa bututu, su na barna a yankin Neja-Delta.

A halin yanzu, gangunan danyen man da Najeriya ta ke fitarwa a kullum bai wuce miliyan 1.49 ba. Ya kamata a ce adadin gangunan ya zarce haka.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Layin man NNPC
Wani layin mai Hoto: businesspost.ng
Asali: Facebook

“Abin da ke faruwa bai da alaka da dokar PIA. Zallar aikin wasu barayi ne; masu fasa bututu sun nakasa harkar hako danyen mai.”
“Sun jefa mu a wani mawuyacin hali, sun kai mu cikin yanayin da mu ka samu kanmu. Ganguna miliyan 1.9 muke hakowa kullum.”
“Idan ka yi asarar ganguna 200, 000 a duk rana, ko da an yi lissafin farashin ganga a $65 ne, mun rasa kusan $1bn daga Junairu zuwa Maris.”

Kara karanta wannan

Neman kujerar Shugaban kasa ya barka Atiku, Saraki da ‘Yan takarar PDP, kai ya rabu 3

“Mun yi asarar kimanin ganguna 250, 000 ne a duk rana, kuma farashin mai a kasuwa yau ya kai $100, kenan har mun rasa kusan $1.5bn

An rahoto Kyari ya na fadawa ‘yan majalisa cewa abin ya yi muni a farkon Maris na 2022, inda ba a iya samun ko sisi daga kudin danyen man kasar ba.

Dokubo Asari v Nyesom Wike

An ji Alhaji Mujaheed Dokubo-Asari ya ce bai ganin cewa Gwamna Nyesom Wike ya dace ya rike Najeriya. Asari ya bayyana wannan ne da aka yi hira da shi.

Mujaheed Dokubo-Asari wanda ya taba jagorantar kungiyar tsagerun Niger Delta Peoples Volunteer Force na kasa, ya caccaki Wike da kuma Peter Obi.

Asali: Legit.ng

Online view pixel