Komai ya na iya faruwa a 2023 – Kwankwaso ya tanka masu rade-radin sake shiga APC

Komai ya na iya faruwa a 2023 – Kwankwaso ya tanka masu rade-radin sake shiga APC

Rade-radi su na ta yawo a game da sauya-shekar Rabiu Musa Kwankwaso daga PDP zuwa jam’iyyar APC

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya amsa wannan tambaya da kan sa a wata doguwar hira da ya yi kwanan nan

Punch ta tambaye shi ko da gaske ya na shirin shiga APC idan an karbe ta daga hannun Abdullahi Ganduje

Abuja - Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyanawa Punch cewa a harkar siyasa komai ya na iya faruwa, ya kuma bayyana akidarsa da irin burinsa.

Hadimin 'dan siyasar, Saifullahi Muhammad Hassan ya tsakuro wannan hira a shafinsa na Facebook.

“A siyasa komai mai iya yiwuwa ne. Ba mu bukatar makiya na din-din-din, abin da muke so shi ne masoya na din-din-din, wannan na da muhimmanci.”

Kara karanta wannan

Yadda ɗan gani kashenin Buhari ya koma Kwankwasiyya bayan ƴan bindiga sun sace ƴan uwansa 5

“Masoya mu ke nema, zai ba ka sha’awa cewa a cikin wadanda muka fara siyasa da su shekaru 30 da suka wuce, wasu su na raye, kuma mu na nan tare.”

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

“Har ma wadanda suka rasu shekaru 30 da suka wuce zuwa yanzu su na cikin ranmu, shekara- shekara mu kan samu danginsu, mu yi masu wani abu.”
“Saboda haka a zaben 2023, na yi imani cewa abubuwa da yawa za su iya faruwa.” – Kwankwaso.
Sanata Rabiu Musa Kwankwaso
Tsohon shugaban PDP, Saraki da Kwankwaso kafin zaben 2019 Hoto: @SaifullahiHon
Source: Twitter

Sai yadda kotun koli tayi da PDP

A game da komawa jam’iyyar APC da ya bari a 2018, tsohon Sanatan na Kano ta tsakiya yace a halin yanzu makomar jam’iyyar PDP ta na ga kotun koli.

“PDP ta shirya zaben shugabanninta, shakka-babu tsohon shugaban jam’iyya na kasa, Uche Secondus ya na kotu, kuma kotun koli za ta yi hukunci.”
“Hukuncin da kotun koli za tayi kwanan nan zai yi tasiri a kan makomar jam’iyyar (PDP). Haka zalika matakin da shugabannin jam’iyya suka zartar.”

- Kwankwaso

Kara karanta wannan

Ina goyon bayan Buhari kan kin sanya hannu a dokar zabe, Sanata Adamu

Kwankwaso wanda yayi gwamna sau biyu a Kano yace jam’iyya ta na iya biyewa gwamnoninta 13, tayi watsi da maganar duk sauran ‘ya ‘ya da magoyanta.

A gefe guda kuma, ‘dan siyasar ya bada shawarar cewa a ajiye girman kai, a tafi da kowa, yace wannan shi ne zai taimakawa jam’iyyun siyasa a wajen zabe.

A cewar Kwankwaso, ita ma APC ta na yin irin na ta shirin wanda idan tayi kuskure za ta auka cikin rigimar da ta fi ta PDP, yace burinsa a samu shugaba na gari.

Mu na lale da Kwankwaso - Babafemi Ojudu

A jiya ne aka ji Hadimin shugaban kasa, Babafemi Ojudu yace zuwan Kwankwaso APC zai amfane su domin shi gawurtaccen ‘dan siyasa ne mai jama’a tare da shi.

A gefe guda, Mai magana da yawun bakin tafiyar Kwankwasiyya, Sunusi Bature Dawakin Tofa yace jita-jitar sauya-shekan duk ba su da asali ko tushen kamawa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng