Sakin Nnamdi Kanu: Sowore, 'Yan Zanga Zanga Sun Ruga da Gudu bayan Fara Harbi
- Rundunar ‘yan sanda da wasu jami’an tsaro sun tarwatsa masu zanga-zangar neman a saki Nnamdi Kanu da harsasai
- Tsohon ɗan takarar shugaban kasa, Omoyele Sowore, ne ya jagoranci masu zanga-zangar a wasu sassa na birnin tarayya Abuja
- Jami’an tsaro daga ‘yan sanda, DSS, NSCDC da sojojin fadar shugaban kasa sun tsaurara tsaro a manyan wurare a birnin Abuja
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
FCT, Abuja - An samu rudani a Abuja yayin da jami’an tsaro suka tarwatsa masu zanga-zangar neman a saki shugaban ƙungiyar IPOB da ake tsare da shi, Nnamdi Kanu.
Masu zanga-zangar sun ruga da gudu bayan jami’an tsaro sun bude wuta da harsasai domin tarwatsa taron.

Source: Facebook
Daily Trust ta wallafa cewa zanga-zangar da Omoyele Sowore ya jagoranta ta gudana ne da sanyin safiya a kusa da hedkwatar ma’aikatar harkokin mata a babban birnin tarayya, Abuja.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Rahotanni sun bayyana cewa jami’an tsaro daga rundunar ‘yan sanda, Hukumar DSS da NSCDC ne suka tsaurara tsaro a yankin tun ranar Lahadi.
Yadda aka fita zanga zangar Nnamdi Kanu
Kafin jami’an tsaro su fara bude wuta, masu zanga-zangar sun yi tattaki zuwa kusa da kotun daukaka kara inda suka rika rera wakoki da kira da a saki Nnamdi Kanu.
Wasu daga cikinsu sun bayyana cewa zanga-zangar nasu ta lumana ce, amma sun yi mamakin yadda jami’an tsaro suka fara kai musu farmaki.
Punch ta wallafa cewa masu zanga-zangar sun fara ja da baya bayan sun ji karar harsasai daga bangarori daban-daban.
Wasu daga cikin su sun bayyana cewa a farkon lokacin sun dauka barkonon tsohuwa ne za a yi amfani da shi, amma sai suka fahimci harsasai ake harbawa.
Maganar Sowore kafin ya ruga da gudu
Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, Omoyele Sowore, wanda ya jagoranci zanga-zangar, ya yi kira ga jami’an tsaro da su mutunta ‘yancin jama’a na yin zanga-zanga cikin lumana.
Ya ce:
“Kada ku yi amfani da barkonon tsohuwa ko harsasai a kanmu! Ku mutunta doka! Muna da ‘yancin yin zanga-zanga — mu ‘yan Najeriya ne.”
Masu zanga-zangar sun ce manufarsu ita ce jan hankalin gwamnati kan ci gaba da tsare Nnamdi Kanu duk da umarnin kotu da ke bukatar a sake shi.

Source: Facebook
Kafin su ruga da gudu, sun bayyana wa jami'an tsaro cewa ba su da niyyar tada tarzoma ko yin barna.
Halin da ake ciki bayan zanga-zanga
Bayan tarwatsa zanga-zangar, an ci gaba da ganin motocin yaƙi da na sulke daga rundunar Guards Brigade da ‘yan sanda suna sintiri a yankin.
Rahotanni sun ce an kafa shingaye a hanyoyin da ke kaiwa fadar shugaban ƙasa, Majalisar Dokoki ta Kasa, Kotun Daukaka Kara da kuma Eagle Square.
A halin yanzu, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa kan harbe-harben ba, sai dai ganau sun ce wasu daga cikin masu zanga-zangar sun samu raunuka yayin gudu daga wurin.
Ana bincike kan juyin mulki a Najeriya
A wani rahoton, kun ji cewa wasu bayanai sun nuna cewa ana cigaba da bincike kan zargin juyin mulki da aka ce an shirya a Najeriya.
Wata majiya ta ce hukumomi sun saka ido a kan wani tsohon gwamna daga Kudancin Najeriya kan zargin yana da hannu a lamarin.
Bayan saka ido da ake a kan tsohon gwamnan, rahotanni sun ce za a gayyace shi ya amsa tambayoyi idan aka samu yana da alaka da yunkurin juyin mulkin.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Asali: Legit.ng


