Wutar Lantarki Ta Samu Matsala, Mutane Za Su Shiga Duhu a Jihohi 4 a Najeriya

Wutar Lantarki Ta Samu Matsala, Mutane Za Su Shiga Duhu a Jihohi 4 a Najeriya

  • Turken wutar lantarki da ke raba wuta zuwa jihohin Ribas, Kuros Riba, Bayelsa da Akwa Ibom ya samu matsala a daren Asabar
  • Kamfanin TCN ya bayyana cewa tuni injiniyoyinsa suka fara aiki domin gano asalin matsalar da gyara ta cikin gaggawa
  • TCN ya bai wa daukacin jama'ar yankin da wannan lamari ya shafa hakuri, ya na mai cewa ana gama gyara za a sako masu wuta babu bata lokaci

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Aba - Kamfanin Raba Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) ya bayyana cewa babban turken wuta dake Aba/Itu ya samu matsala.

Kamfanin TCN ya ce wutar da ake rabawa ta kan turken mai karfin 132KV ta katse, lamarin da zai jefa wasu yankuna cikin duhu har zuwa lokacin da za a gyara.

Layukan wutar lantarki.
Hoton turakun da ke raba wutar lantarki a Najeriya Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Hakan dai na kunshe ne a wata sanarwa da mai magana da yawun kamfanin TCN, Ndidi Mbah, ya fitar a ranar Lahadi, kamar yadda The Cable ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Atiku ya sake yi wa gwamnatin Tinubu saukale, ya fadi abin da ta gaza magancewa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An dauke wuta a Akwa Ibom da jihohi 3

Sanarwar ta ce katsewar layin wutar ta faru ne sakamakon gocewar layin wuta wanda ya dakatar da wutar da ake bai wa Kamfanin Raba Wutar Lantarki na Fatakwal (PHED) da kuma na Jihar Akwa Ibom.

Kamfanin TCN ya bayyana cewa jihohin da PHED ke bai wa wutar lantarki sun haɗa da Bayelsa, Kuros Riba da Ribas.

Wace matsala aka samu a turken wutan?

A ruwayar jaridar Punch, sanarwar ta ce:

"Kamfanin TCN na sanar da al'umma cewa wuta ta dauke a turken lantarki na Aba/Itu a ranar Asabar, 13 ga Satumba, 2025, da misalin ƙarfe 1:03 na dare sakamakon tsallaken layin wuta."
“Hakan ya kawo cikas ga wutar lantarki da ake bai wa PHED tare da wutar da ake samarwa a Jihar Akwa Ibom.
"Ma’aikatanmu na sashen gyare-gyare sun riga sun fara aiki da gaggawa don gano matsalar da gyara ta domin dawo da wuta a yankunan da abin ya shafa.”

Kara karanta wannan

Rikicin NUPENG da Dangote: Kungiyar kiristoci ta fara azumin kwanaki 14

Kamfanin TCN ya bai wa jama’a hakuri bisa dauke wutar da aka yi sakamakon wannan matsala da ta faru tare da tabbatar da cewa za a dawo da wuta da zarar an kammala gyara.

Ma'aikatan TCN.
Hoton wasu ma'aikata suna gyaran wutar lantarki Hoto: TCN
Source: UGC

Yadda TCN ke fama da lalacewar wuta

TCN ya kuma tunatar da cewa a ranar 8 ga Satumba, an samu guguwa da hadari da ta yanke layin wutar 132KV Otukpo–Nsukka–New Haven, wanda ya haddasa gobara.

Sanarwar ta ce wannan lamarin ya yi sanadiyyar ƙonewar wani gida da aka gina ƙarƙashin layin wutar, ya ƙone wata mota da aka ajiye a wurin, tare da halaka shanu guda biyu da suka faɗa a layin.

Za a daina dauke wutar lantarki a Najeriya

A wani labarin, kun ji cewa Gwamnatin Tarayya ta yi ikirarin cewa nan ba da jimawa ba yan Najeriya za su ga an daina dauke wutar lantarki kwata-kwata.

Ministan Makamashi, Adebayo Adelabu ya ce ƙoƙarin da Gwamnatin Tarayya ke yi ya fara haifar da sakamako mai kyau domin wutar Lantarki da ake samarwa yanzu ta.zarce ta baya.

Ya ce gwamnati na samar da hasken wutar lantarki a jami’o’i, asibitocin koyarwa, cibiyoyin kiwon lafiya, hukumomin gwamnati da garuruwa.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262