Jerin Manya da 'Yan Siyasar da Suka Yi Magana kan Lafiyar Shugaba Tinubu
Abuja - Batun lafiyar shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ne babban abin da aka fi tattaunawa a kai a Najeriya a yan kwanakin nan.
CHECK OUT: Education is Your Right! Don’t Let Social Norms Hold You Back. Learn Online with LEGIT. Enroll Now!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Mutane, musamman a kafafen sada zumunta sun rika yada labarin cewa Shugaba Tinubu ba shi da lafiya, kuma hakan ne ya sa aka daina ganinsa a bainar jama'a.

Asali: Twitter
Yadda aka fara yada labarin lafiyar Tinubu
Jita-jitar ta samo asali ne daga wani rahoto da cibiyar ICIR ta wallafa, wanda ya ambato wasu majiyoyi na cewa Tinubu ba shi da lafiya har an fara shirin fitar da shi kasar waje.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Rahoton ya yi ikirarin cewa rashin lafiyar da Shugaba Tinubu ke fama da ita ce ta sanya aka daina ganinsa a wuraren taruka da ya kamata ya halarta.

Kara karanta wannan
Ana batun rashin lafiyar Tinubu, Gwamna Radda zai tafi jinya domin duba lafiyarsa
A cewar majiyoyin da cibiyar ta tattara, mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ne ke wakiltarsa, lamarin da ya kara jefa shakku a zukatan yan Najeriya.
Manyan da suka yi magana kan lafiyar Tinubu
Tun bayan bullar wannan labari, fadar shugaban kasa, manya da yan siyasa da dama sun fito sun karyata, wasu ma sun samu ganawa da Tinubu a Aso Rock.
A wannan rahoton, Legit Hausa ta tattaro maku duk wadanda suka yi magana kan lafiyar Shugaba Tinubu da kuma abin da suka ce, ga su kamar haka:
1. Kakakin shugaban kasa, Bayo Onanuga
Mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga ya karyata rahoton rashin lafiyar mai girma Tinubu.
Onanuga ya shaidawa cibiyar ICIR cewa Tinubu na cikin koshin lafiya kuma yana gudanar da aikinsa sabanin labarin karya da aka ba su.

Asali: Twitter
Yayin da Daily Trust ta tuntube shi don jin gaskiyar labarin, kakakin shugaban kasar ya bukaci a yi watsi da jitar-jitar wacce ya bayyana da mara tushe.

Kara karanta wannan
"Ina da tabbaci," Bwala ya hango yadda za ta kaya tsakanin Jonathan da Tinubu a 2027
Da aka tambaye shi kan dalilin rashin fitowar Tinubu bainar jama'a, Bayo Onanuga ya amsa da cewa shugaban na da yancin gudanar da ayyuka daga gida.
"Ba abin da ke damun shugaban kasa, yana cikin koshin lafiya, doka ta ba shi yancin yin aiki daga gida ko wani wuri da ya ga dama, ina tabbatar maku da cewa lafiyarsa kalau," in ji shi.
2. Sanata Orji Uzor Kalu
Sanata mai wakiltar mazabar Abia ta Arewa a majalisar dattawa, Orji Uzor Kalu ya musanta labarin da ake yadawa game da rashin lafiyar Shugaba Tinubu.
Kalu, tsohon gwamnan Abia ya ce ya yi magana da shugaban kasa a wayar salula a daren ranar Litinin 11 ga watan Agustan 2025.
Ya tabbatar wa yan Najeriya cewa Tinubu na cikin koshin lafiya, yana mai cewa gajiya ce kawai wacce kowa na iya jin kasala har ya gaza fita wurin aiki.

Asali: Facebook
A wani faifan bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Sanata Kalu ya ce:

Kara karanta wannan
Ana jita jitar rashin lafiya, Tinubu ya yi magana, ya fadi gwamnonin da zai yi alaƙa da su
"Na yi magana da shi (Shugaba Tinubu) awanni biyu da suka wuce kuma yana cikin koshin lafiya, gajiya ce kawai yanzu yana shirye-shiryen zuwa Japan, sannan zai tsaya a Brazil."
3. Hadimin shugaban kasa, Abdul'aziz Abdul'aziz
Mai ba shugaban kasa shawara ta musamman kan harkokin jaridu, Abdulaziz Abdulaziz ya ce gaba daya rahotannin rashin lafiyar Tinubu ba gaskiya ba ne.
Ya ce jita-jitar da ake yadawa abin dariya ce duba da yadda ake yada labarin da yake karya mara tushe balle makama.

Asali: Facebook
"Dariya abin yake ba mu domin mun san abin da ake yadawa karya ce. Shugaban kasa mutum ne dan adam kamar kowa, kamar ni da kai, zai iya yin rashin lafiya, amma a yanzu dai lafiyarsa kalau," in ji shi.
Hadimin shugaban kasar, Abdul'aziz ya yi wannan bayani ne yayin wata tattaunawa da DCL Hausa kan batun lafiyar Bola Tinubu.
4. Jagora a APC, Farouk Adamu Aliyu

Kara karanta wannan
Magana ta kare, bidiyon Shugaba Tinubu ya bayyana ana tsaka da jita jitar ba shi da lafiya
Tsohon dan majalisar wakilai kuma jigo a APC, Farouk Adamu Aliyu ya bayyana cewa ya samu ganin Shugaba Tinubu kuma babu wata alamar da ke nuna ba shi da lafiya.
A cewarsa, ya shafe kusan mintuna 30 suna tattaunawa da shugaban kasa, amma bai ga wani sauyi daga yadda ya saba ganinsa ba.

Asali: Twitter
A wata hira da DCL Hausa, jigon ya ce cuta tana iya hawa kan kowa, amma dai Shugaba Tinubu lafiyarsa kalau.
Farouk Aliyu ya ce:
"Na farko dai cuta tana kan kowa, amma a yadda na gan shi, babu alamar ciwo sai dai dattijantaka wanda idan shekaru suka cimma mutum zai samu irin wannan.
"A cikin maganganun da muka yi, ya gaya mani cewa zai yi tafiya zuwa wata kasa, daga nan ya wuce wata kasa, ka ga mutum mara lafiya zai yi irin wannan tafiye-tafiye?"
5, Gwamna Soludo na jihar Anambra
Gwamnan jihar Anambra, Charles Chikwuma Soludo, na daya daga cikin manyan mutanen da suka ziyarci Shugaba Bola Ahmed Tinubu yayin da ake rade-radin ba shi da lafiya.
A rahoton da The Cable ta kawo, gwamnan ya bayyana cewa Shugaba Tinubu na cikin koshin lafiya sabanin yadda mutane ke yadawa.

Asali: Twitter
Da yake hira da manema labarai a fadar shugaban kasa bayan ganawa da Tinubu a ofishinsa, Soludo ya ce:
"Shugaba Tinubu yana cikin farin ciki, yana cikin ƙoshin lafiya, yana karɓar baƙi da sauran aikace-aikace."
Shugaba Tinubu zai yi tafiya zuwa kasashe 2
A wani labarin, kun ji cewa Shugaba Bola Tinubu zai bar Najeria zuwa wasu kasashe biyu domin halartar taruka a ranar Alhamis, 14 ga watan Agusta, 2025.
Mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya ce Tinubu zai tafi Japan da Brazil domin halartar taruka da ganawa da shugabanni.
Ana sa ran ministoci da wasu manyan jami'an gwamnatin Najeriya za su raka shugaban kasar zuwa kasashen guda biyu.
Asali: Legit.ng