Gwamnatin Tinubu Ta Yi Wa Ƴan Najeriya Albashir da ASUU Ke Shirin Rufe Jami'o'i

Gwamnatin Tinubu Ta Yi Wa Ƴan Najeriya Albashir da ASUU Ke Shirin Rufe Jami'o'i

  • Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka tana koƙarin dakile sabon yunkurin malaman jami'a na shiga yajin aiki
  • Karamar ministar kwadago, Hon. Nkeiruka Onyejeocha ce ta bayyana hakan a wani taron kiwon lafiya da ta halarta a jihar Abia
  • Ta ce shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya kudiri aniyar saita tattalin arziki ta hanyar tsare-tsaren da ya ɓullo da su a gwamnatinsa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abia - Ƙaramar minsistar kwadago da samar ayyukan yi, Hon. Nkeiruka Onyejeocha ta ce gwamnatin tarayya na koƙarin dakile yunƙurin ASUU na shiga yajin aiki.

Ta ce gwamnatin ba za ta bari kungiyar malaman jami'o'i ta ƙasa watau ASUU ta shiga yajin aiki ba, za ta yi duk mai yiwuwa wajen biya mata buƙatunta.

Kara karanta wannan

NNPP na fama da rikici a Kano, Ganduje ya sake yi wa jam'iyyar adawa lahani

Bola Tinubu da shugaban ASUU.
Gwamnatin tarayya ta fara kokarin lallaba ASUU ka da ta tsunduma yajin aiki Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ASUU
Asali: Twitter

Minista ta hango amfanin manufofin Tinubu

Onyejeocha ta kuma ƙara da cewa manufofin shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu za su magance matsalolin tattalin arziki tun daga tushe, Vanguard ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewarta, nan gaba ƴan Najeriya za su amfana da tsare-tsaren Tinubu duk a yanzu suna fuskankar matsi.

Ministar ta yi wannan jawabi ne a lokacin da take amsa tambayoyi daga manema labarai a wurin bikin kiwon lafiya karo na 17 a Isuochi, jihar Abia.

Wane mataki gwamnati ta ɗauka kan ASUU? 

Hon. Nkeiruka Onyejeocha ta bayyana cewa nan ba da daɗewa ba za a warware dukkan batutuwan da ASUU take kuka a kansu, in ji Punch.

A makon jiya ne ASUU ta ba gwamnatin tarayya wa'adin kwanaki 14 ta biya bashin da malaman jami'o'i suka biyo a lokacin yajin aiƙin 2020.

Kara karanta wannan

"Na cancanta," Sanatan APC ya bayyana shirinsa na neman zama shugaban ƙasa a 2027

Kungiyar ta kuma bukaci gwamnati ta cire mambobinta daga tsarin biyan albashi na IPPIS, sannan a maida su kan wanda suka gabatar watau UTAS.

Gwamnati ta kusa shawo kan ASUU

Da take jawabi, ƙaramar ministar kwadagon ta ce:

"Dangane da batun barazanar ASUU na shiga yajin aiki, mun zauna mun tattauna kuma ina da tabbacin nan ba da jimawa ba za a warware komai.
"Game da yajin aikin da ke kunno kai kuma mun zauna da ƴan kwadago, mun fahimci juna sannan mun gaya masu halin da ƙasar nan ke ciki."

ASUU ta shiga yajin aiki a Gombe

A wani labarin kuma kungiyar malaman jami'o'i ta kasa (ASUU) a jami'ar jihar Gombe ta tsunduma yajin aiki sakamakon rashin biya mata bukatu.

Shugaban ASUU na jami'ar jihar Gombe, Dakta Salihu Sulaiman Jauro ya bayyana abubuwan da gwamnati ta gaza yi musu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262