Cuta Ta Ɓarke a Jihar Borno bayan Ambaliyar Ruwan da Ta Afku, Bayanai Sun Fito

Cuta Ta Ɓarke a Jihar Borno bayan Ambaliyar Ruwan da Ta Afku, Bayanai Sun Fito

  • Gwamnatin Borno ta bayyana cewa an samu ɓullar cutar kwalara a wasu ƙananan hukumomi sakamakon ambaliyar ruwa
  • Kwamishinan lafiya, Farfesa Baba Gana ya ce gwamnati ta fara kokarin yaƙar cutar tun da wuri domin daƙile yaɗuwarta
  • Ya ce ana zargin cutar ta ɓarke ne sanadin mummunar ambaliyar ruwan da aka yi a makonnin da suka gabata a wasu sassan jihar Borno

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Borno - Gwamnatin jihar Borno ta tabbatar da ɓullar cutar kwalara watau amai da gudawa sakamakon ambaliyar ruwan da ta afku kwanakin baya.

Kwamishinan lafiya na Borno, Farfesa Baba Gana shi ne ya bayyana hakan a asibitin ido da ke Maiduguri ranar Alhamis.

Kara karanta wannan

"Abin ya fara yawa": Haɗarin jirgin yan Maulidi ya jawo hankalin shugaba Tinubu

Ambaliyar ruwan Maiduguri.
Gwamnatin Borno ta fara ɗaukar mataki bayan ɓarkwar cutar kwalara Hoto: Contributor
Asali: Getty Images

Ya ce ma'aikatar ta tura samfurin mutum 200 domin gwaji kuma sakamakon ya nuna mutane 17 daga cikin sun kamu da cutar kwalara, Channels tv ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Me ya jawo ɓarkewar kwalara a Borno?

A cewarsa, ɓarkewar cutar a wannan karon yana da nasaba da ibtila'in ambaliyar ruwan da ta afku a Maiduguri da wasu sassan kananan hukumomin jihar

Farfesa Baba Gana ya bayyana cewa a halin yanzu an gano cutar ta ɓulla a ƙananan hukumomin Jere, Mafa, Konduga, Dikwa da MMC

Ya ce duk da babu wanda cutar ta kashe kawo yanzu amma ana samun ƙaruwar kamuwa da ita a kananan hukumomi da dama.

Baba Gana ya ƙara da cewa zuwa yanzu su na da rahoton waɗanɗa ake zargin sun kamu da cutar har mutum 451 amma mutum 17 ne kaɗai aka tabbatar.

Wane mataki gwamnatin Borno ta ɗauka?

Kara karanta wannan

Gwamna ya ba da hutu a ranakun Alhamis da Juma'a a jiharsa, bayanai sun fito

Wannan ya sa gwamnatin Borno karkashin jagorancin Gwamna Babagana Umaru Zulum ta sanar da fara ɗaukar mataki cikin gaggawa don daƙile yaɗuwar cutar.

A cewar gwamnatin, ta tanadi allurar rigafin cutar guda 400,000 waɗanda za a yi amfani da su domin kare sauran al'umma.

Haka nan kuma ƙungiyoyi masu zaman kansu kamar WHO da MSF sun fara tanadar wurare da kayan aiki domin killace waɗanda suka kamu da cutar.

Gwamna Zulum ya ziyarce wuraren ambaliya

A wani labarin kuma kun ji cewa Gwamna Babagana Umara Zulum ya ziyarci wasu wuraren da ambaliya ta yi gagarumar barna a jihar Borno.

Mai girma gwamnan ya yi takaicin yadda wasu mutane su ka gina gidaje a gabar ruwa, wanda haka. ya hana ruwa bin hanyarsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262