1 ga Oktoba: Gwamna Ya Ba Matasa Shawara kan Shirya Zanga Zanga

1 ga Oktoba: Gwamna Ya Ba Matasa Shawara kan Shirya Zanga Zanga

  • Gwamnatin jihar Adamawa ta yi kira ga mutanen jihar da ka da su shiga zanga-zangar da aka shirya gudanarwana ranar 1 ga watan Oktoban 2024
  • Babban mai ba gwamnan jihar shawara na musamman kan zaman lafiya da tsaro ya buƙaci iyaye da ka da su bari ƴaƴansu su shiga zanga-zangar
  • Ahmed Lawan ya bayyana cewa jihar ba ta taɓa amfana daga zanga-zangar da aka taɓa yi a baya ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Adamawa - Gwamnatin jihar Adamawa ƙarƙashin jagorancin Gwamna Ahmadu Fintiri, ta yi kira ga al'ummar jihar da ka da su shiga zanga-zangar da aka shirya ranar, 1 ga watan Oktoban 2024.

Gwamnatin ta buƙaci al'ummar jihar musamman matasa da ka da su shiga zanga-zangar wacce aka shirya gudanarwa.

Kara karanta wannan

"Na shirya rantsewa da Alƙur'ani ban taɓa satar ko kwabo ba," Tsohon gwamna El Rufai

Gwamnatin Adamawa ta bukaci ka da a yi zanga zanga
Gwamnatin Adamawa ta bukaci ka da matasa su yi zanga zanga Hoto: @AUFintiri
Asali: Facebook

Babban mai ba gwamna Ahmadu Fintiri shawara na musamman kan zaman lafiya da tsaro, Ahmed Lawan ya yi wannan kiran, cewar rahoton jaridar Tribune.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Meyasa gwamnati ba ta son a yi zanga-zanga?

A cikin wata sanarwa da ya fitar, ya bayyana cewa Adamawa ta samu zaman lafiya kuma ganganci ne duk wani mai kishin ƙasa ya yi tunanin cewa zai fito zanga-zanga, rahoton jaridar The Guardian ya tabbatar.

Ahmed Lawan, wanda ya ce jihar Adamawa ba za ta shiga zanga-zangar ba, ya ƙara da cewa jihar ba ta taɓa samun wani amfani ba daga zanga-zangar da aka taɓa yi a baya.

Ya bayyana cewa bai kamata a kawo naƙasu ga manyan ayyukan ci gaba da gwamnatin jihar ke yi saboda zanga-zangar ba.

"Muna kira ga iyaye, ƙungiyiyon addini da su ba ƴaƴansu da mabiyansu shawara ka da su fito zanga-zangar wacce wasu da ba a san ko su wanene ba suka shirya."

Kara karanta wannan

1 ga Oktoba: Kotu ta yanke hukunci kan zanga zangar da ake shirin yi, ta jero wurare 4

"Ya kamata duk wani mai kishin ƙasa nagari yayi watsi da shirin masu zanga-zangar waɗanda ba a san ko su wanene ba."

- Ahmed Lawan

Ƴan sanda sun yi gargaɗi kan zanga-zanga

A wani labarin kuma, kun ji cewa rundunar ƴan sandan jihar Kano ta gargadi masu shirin gudanar da zanga-zanga a ranar 1 ga watan Oktoba, 2024.

Rundunar ta ja kunnen masu shirin fita kan tituna da cewa ba za ta lamunci karya doka da oda da sunan zanga-zangar tsadar rayuwa ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng