A Kwana da Shiri: Ana Fama da Ambaliya a Borno, NiMET Ta Yi Hasashe Mai Firgitarwa

A Kwana da Shiri: Ana Fama da Ambaliya a Borno, NiMET Ta Yi Hasashe Mai Firgitarwa

  • Yayin da al'ummar Borno ke fama da matsalar ambaliya da ta nemi shafe Maiduguri, hukumar hasashen yanayi (NIMET) ta yi sabon hasashe
  • A sabon hasashen, NIMET ta bayyana cewa za a samu mamakon ruwa kamar da bakin kwarya hadi da tsawa na kwanaki uku a jere
  • Jihohin da NIMET ta bayyana cewa za a samu ruwa da tsawa sun hada da Borno, Adamawa, Taraba, Yobe, Katsina, Sokoto da Kaduna

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT, Abuja - Hukumar hasashen yanayi ta kasa (Nimet) ta gargadi mazauna kasar nan da cewa za a samu mamakon ruwan sama hadi da tsawa daga ranar Laraba zuwa Juma'a.

Kara karanta wannan

Ambaliya: Mutane kusan 50 sun rasu, gidaje 6000 sun lalace a garuruwa 200 a Kano

Hukumar ta fitar da sabon hasashen ne yayin da jama'ar Maiduguri a jihar Borno da wani sashe na Bauchi ke fama da matsananciyar ambaliya.

Ambaliya
An yi sabon hasashen mamakon ruwa a Najeriya Hoto: Umar Yahaya Ahmad
Asali: Facebook

Jaridar Vanguard ta wallafa cewa wasu daga cikin jihohin Arewa da su ka hada da Borno, Adamawa, Taraba, Yobe, Katsina, Sokoto da Kaduna za su fuskanci ruwa da tsawa a safiyar Laraba.

Jihohin da za a fuskanci mamakon ruwa

Sauran jihohin da NiMET ta yi hasashen ruwa kamar da bakin kwarya sun hada da wasu sassan Kano, Borno, Katsina, Adamawa, Kaduna, Taraba, Zamfara, Kebbi, da Jigawa.

A yankin Arewa ta Tsakiya kuma akwai jihohin Nasarawa, Neja, Binuwai, Kogi, Kwara da Abuja, yayin da ake tsammanin ruwan a Kudanci a jihohin Oyo, da Osun.

Sauran jihohin sun hada da Ekiti, Ogun, Ondo, Lagos, Edo, Delta, Cross River da Akwa Ibom, kamar yadda Solacebase ta wallafa.

Kara karanta wannan

EFCC ta gano musabbabin ta'addanci, an shirya daukar matakai

Ambaliyar ruwa: NiMET ta bayar da shawarwari

Hukumar NiMET ta shawarci jama'a su dauki matakan kare kawunansu yayin da ake sa ran afkuwar ambaliyar ruwa.

NiMET ta ce ana sa ran za a samu iska mai karfi gabanin mamakon ruwan sama, wanda haka ne zai iya kara ta'azzara lamarin.

Ambaliyar ruwa ta mamaye Maiduguri

A baya kun ji cewa madatsar ruwan Alo ta balle a Maiduguri wanda ya jawo ambaliya mafi muni da aka gani a jihar Borno a shekaru 30, inda ruwan ya mamaye gidaje da sauran wurare.

Ambaliyar ta jawo matsaloli da dama inda jami'an lafiya su ka shiga fargabar akwai yiwuwar a samu ballewar cututtuka bayan ruwan ya wanke makabartu da gidan namun daji.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.